• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

De Bruyne Zai Bar Manchester City A Ƙarshen Kakar Wasanni

by Rabilu Sanusi Bena
2 months ago
in Wasanni
0
De Bruyne Zai Bar Manchester City A Ƙarshen Kakar Wasanni
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗan wasan tsakiyar Belgium, Kevin De Bruyne, ya bayyana cewa zai bar Manchester City a ƙarshen wannan kakar wasa, bayan shafe shekaru 10 yana taka leda a ƙungiyar.

Ɗan wasan mai shekaru 33, ya ce kwantiraginsa zai ƙare a bana, kuma lokaci ya yi da zai bar Etihad Stadium.

  • Tinubu Da Kwankwaso Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Dokta Idris Dutsen Tanshi
  • Kasar Sin Na Nuna Damuwa Sosai Kan Harin Intanet Da Aka Kai Mata

Tun daga shekarar 2015 da ya koma ƙungiyar daga Wolfsburg, De Bruyne ya lashe kofuna 16 da suka haɗa da gasar Firimiyar Ingila sau shida da kuma kofin Zakarun Turai a 2023.

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, ya ce De Bruyne “yana daga cikin mafiya ƙwarewa a matsayin ɗan wasa a tsakiya da duniya ta taɓa gani.”

De Bruyne ya buga wasanni 413 tare da zura ƙwallaye 106 a City.

Labarai Masu Nasaba

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

A wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, ya ce: “Ko muna so ko ba mu so, lokaci ya yi da za mu yi bankwana.”

Ƙungiyar Manchester City ta ce za ta shirya wani bikin bankwana na musamman domin girmama ɗan wasan kafin kakar ta ƙare.

De Bruyne ya koma City daga Wolfsburg a kan fan miliyan 55, kuma ya taimaka sosai wajen nasarorin da ƙungiyar ta samu, ciki har da lashe kofin Zakarun Turai karo na farko a tarihinta, inda suka doke Inter Milan a wasan ƙarshe a birnin Istanbul.

Sai dai ɗan wasan ya sha fama da rauni a ‘yan shekarun nan, inda ya shafe watanni biyar yana jinya a kakar da ta wuce.

A kakar bana, ya buga wasanni 26 kacal a dukkanin gasa.

De Bruyne, ya fara wasan ƙwallon kafa a kulob din Genk na Belgium, kafin Chelsea ta saye shi a watan Janairu 2012 a kan fan miliyan bakwai.

Ya buga wa Chelsea wasanni tara kacal sannan aka tura shi aro zuwa Werder Bremen, daga nan ya koma Wolfsburg a 2013, kafin komawarsa City.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Barin KungiyaDe BruyneManchester City
ShareTweetSendShare
Previous Post

Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Matakan Harajin Fito Na Amurka Sun Sa Ta Zama Makiyiyar Duniya

Next Post

APC Ce Ke Min Bita-Da-Ƙulli Wajen Yi Min Kiranye – Sanata Natasha

Related

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal
Wasanni

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

20 minutes ago
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona
Wasanni

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

2 days ago
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Wasanni

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

4 days ago
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5
Wasanni

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

5 days ago
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa
Wasanni

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

6 days ago
Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano
Labarai

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

7 days ago
Next Post
Ƙoƙarin Tsige Sanata Natasha Ya Gaza Cika Ƙa’idar Doka – INEC

APC Ce Ke Min Bita-Da-Ƙulli Wajen Yi Min Kiranye - Sanata Natasha

LABARAI MASU NASABA

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.