• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dimbin Ma’adinan Kasar Nan Sun Isa Su Kore Mana Talauci -Minista

by Bello Hamza
1 year ago
in Labarai
0
Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bai kamata Nijeriya ta kasance tana fama da talauci ba, bayan tana zaune a kan dimbin ma’adanai shinfide a sassan kasar nan.

Ministan Ma’adanai, Dakta Dele Alake ya bayyana haka a taron baye kolin ma’adanai da kuma bayar da takardar shaida ga daliban da suka horo a kan sarrfa ma’adanai da kamfanin MinDiber ta dauki nauyi gabatarwa wanda aka gudanar a Abuja ranar Alhamis da ta gabata.

  • Gwamnatin Kwara Ta Tasa Keyar Mabarata 158 Zuwa Jihohinsu Na Asali
  • Matsalolin Tsaro Da Ambaliya: ‘Yan Nijeriya Sun Sayo Abinci Daga Waje Na Tiriliyan 3 – CBN

Dakta Alake ya kuma ce, kawo shirin kera sarkar gwalagwalai tamkar kawo arziki cikin gida Nijeriya ne.

Ministan ya kuma bayar da kayan fara aiki ga wadanda suka koyi yadda ake kera gwalagwalan, ya ce mu su yanzu da aka basu kayan aiki tamkar an samar musu da hanyar cin abinci ne domin bunkasa rayuwarsu, ya kuma bukaci su bayar da nasu gudummawr domin bunkasa sashin hakar ma’adanai domin samun nasarar kasa gaba daya.

Ya kuma ce, “Babu wata jiha a kasar nan da ba ta da wani nau’in ma’adani da Allah ya shinfida a jihar, “a kan haka ban ga dalilimu na fama da talauci ba” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

“Indan da mun yi abin da ya kamata a shekarun baya, inda mun mayar da hankalinmu zuwa bangaren ma’adanai, da bangaren ya isa ya rike mana tattalin arziki. Amma sai muka ki saboda muna ganin an samu man fetur sai muka kulle idonmu daga abubuwa kamar gemstone, gwalagwalai da abin da ya shafi harkar gona.

Ya ce, a halin yanzu duniya tana nesa-nesa daga man fetur tana komawa abin da ya shafi wasu makamashi musamman ganin yadda fetur ke kara ta’azzarar karuwar dumamar yanayi.

A jawabinsa, shugaban kamfanin MinDiber, Injiniya Sallim Salaam ya ce, an shirya taron ne domin mika jinjina ga ‘yan Nijeriya da suka koya tare da kwarewa wajen kera gwala-gwalai, irin gwalagwalan da za su yi gogayya da irin wadanda ake kerawa a kashen duniya.
Ya ce, taron ya kuma zama fagen da wadanda suka samu horon za su baje kolin irin kayayyakin da suka kera domin duniya ta gani, ya kuma yaba da irin kokarin su a wannan fagen.

A kan haka ya kuma mika godiyarsa ga babban sakataren ma’aikatar ma’adanai a kan irin goyon bayan da suka samu wajen samun nasarar bikin baje kolin ya kuma yi alkawarin ci gaba da tallafa wa matasa don su bunkasa rayuwarsu.

Ya kuma nemi matasan da suka samu horon su koma jihohinsu domin su horars da wasu matasan, ta yadda suma za su samu abin dogaro da kai.

A nata jawabin, babbar sakatariyar ma’aikatar ma’adanai, Dakta Mary Ogbe, ta yi kira ne ga gwamnonin jihohi su tallafa wa matasan da kudaden da za su fadada harkokinsu tare da kuma horas da wasu matasan. Ta haka za a tabbatar da an hau hanyar yaki da talauci da zaman kashe wando a tsakanin matasan Nijeriya.

Taron ya samu halartar manyan ma’aikatan gwamnati, masu ruwa da tsaki a bangaren ma’adanai da sauran al’umma, inda suka yaba da irin ayyukan da matasan suka gabatar.

Daga cikin matasa 96 da suka fara horon matasa 36 ne suka samu nasarar kammala horon. Daya daga cikin matasan mai suna Felicitas Ella daga Jihar Kros Ribas ta mika godiyarta ga kamfanin da ya dauki nauyin horars da su ta kuma yi alkawarin aiki da abin da ta koya yadda kamata ta kuma yi alkawarin horas da wasu matasan a jihar su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zan Gaggauta Rattaba Hannu A Hukuncin Wanda Ya Kone Mutane A Masallaci – Gwamnan Kano

Next Post

Gwamnan Kano Ya Bada Umarnin Kamo Tsohon Sarkin Kano Aminu Ado Bayero

Related

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

2 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

3 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

4 hours ago
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano
Labarai

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

4 hours ago
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
Labarai

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

8 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

9 hours ago
Next Post
Gwamnan Kano Ya Bada Umarnin Kamo Tsohon Sarkin Kano Aminu Ado Bayero

Gwamnan Kano Ya Bada Umarnin Kamo Tsohon Sarkin Kano Aminu Ado Bayero

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.