• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dimbin Ma’adinan Kasar Nan Sun Isa Su Kore Mana Talauci -Minista

by Bello Hamza
1 year ago
in Labarai
0
Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bai kamata Nijeriya ta kasance tana fama da talauci ba, bayan tana zaune a kan dimbin ma’adanai shinfide a sassan kasar nan.

Ministan Ma’adanai, Dakta Dele Alake ya bayyana haka a taron baye kolin ma’adanai da kuma bayar da takardar shaida ga daliban da suka horo a kan sarrfa ma’adanai da kamfanin MinDiber ta dauki nauyi gabatarwa wanda aka gudanar a Abuja ranar Alhamis da ta gabata.

  • Gwamnatin Kwara Ta Tasa Keyar Mabarata 158 Zuwa Jihohinsu Na Asali
  • Matsalolin Tsaro Da Ambaliya: ‘Yan Nijeriya Sun Sayo Abinci Daga Waje Na Tiriliyan 3 – CBN

Dakta Alake ya kuma ce, kawo shirin kera sarkar gwalagwalai tamkar kawo arziki cikin gida Nijeriya ne.

Ministan ya kuma bayar da kayan fara aiki ga wadanda suka koyi yadda ake kera gwalagwalan, ya ce mu su yanzu da aka basu kayan aiki tamkar an samar musu da hanyar cin abinci ne domin bunkasa rayuwarsu, ya kuma bukaci su bayar da nasu gudummawr domin bunkasa sashin hakar ma’adanai domin samun nasarar kasa gaba daya.

Ya kuma ce, “Babu wata jiha a kasar nan da ba ta da wani nau’in ma’adani da Allah ya shinfida a jihar, “a kan haka ban ga dalilimu na fama da talauci ba” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

“Indan da mun yi abin da ya kamata a shekarun baya, inda mun mayar da hankalinmu zuwa bangaren ma’adanai, da bangaren ya isa ya rike mana tattalin arziki. Amma sai muka ki saboda muna ganin an samu man fetur sai muka kulle idonmu daga abubuwa kamar gemstone, gwalagwalai da abin da ya shafi harkar gona.

Ya ce, a halin yanzu duniya tana nesa-nesa daga man fetur tana komawa abin da ya shafi wasu makamashi musamman ganin yadda fetur ke kara ta’azzarar karuwar dumamar yanayi.

A jawabinsa, shugaban kamfanin MinDiber, Injiniya Sallim Salaam ya ce, an shirya taron ne domin mika jinjina ga ‘yan Nijeriya da suka koya tare da kwarewa wajen kera gwala-gwalai, irin gwalagwalan da za su yi gogayya da irin wadanda ake kerawa a kashen duniya.
Ya ce, taron ya kuma zama fagen da wadanda suka samu horon za su baje kolin irin kayayyakin da suka kera domin duniya ta gani, ya kuma yaba da irin kokarin su a wannan fagen.

A kan haka ya kuma mika godiyarsa ga babban sakataren ma’aikatar ma’adanai a kan irin goyon bayan da suka samu wajen samun nasarar bikin baje kolin ya kuma yi alkawarin ci gaba da tallafa wa matasa don su bunkasa rayuwarsu.

Ya kuma nemi matasan da suka samu horon su koma jihohinsu domin su horars da wasu matasan, ta yadda suma za su samu abin dogaro da kai.

A nata jawabin, babbar sakatariyar ma’aikatar ma’adanai, Dakta Mary Ogbe, ta yi kira ne ga gwamnonin jihohi su tallafa wa matasan da kudaden da za su fadada harkokinsu tare da kuma horas da wasu matasan. Ta haka za a tabbatar da an hau hanyar yaki da talauci da zaman kashe wando a tsakanin matasan Nijeriya.

Taron ya samu halartar manyan ma’aikatan gwamnati, masu ruwa da tsaki a bangaren ma’adanai da sauran al’umma, inda suka yaba da irin ayyukan da matasan suka gabatar.

Daga cikin matasa 96 da suka fara horon matasa 36 ne suka samu nasarar kammala horon. Daya daga cikin matasan mai suna Felicitas Ella daga Jihar Kros Ribas ta mika godiyarta ga kamfanin da ya dauki nauyin horars da su ta kuma yi alkawarin aiki da abin da ta koya yadda kamata ta kuma yi alkawarin horas da wasu matasan a jihar su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zan Gaggauta Rattaba Hannu A Hukuncin Wanda Ya Kone Mutane A Masallaci – Gwamnan Kano

Next Post

Gwamnan Kano Ya Bada Umarnin Kamo Tsohon Sarkin Kano Aminu Ado Bayero

Related

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

3 hours ago
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

6 hours ago
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
Labarai

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

6 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

8 hours ago
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50
Labarai

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

9 hours ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

9 hours ago
Next Post
Gwamnan Kano Ya Bada Umarnin Kamo Tsohon Sarkin Kano Aminu Ado Bayero

Gwamnan Kano Ya Bada Umarnin Kamo Tsohon Sarkin Kano Aminu Ado Bayero

LABARAI MASU NASABA

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.