ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dimbin Ma’adinan Kasar Nan Sun Isa Su Kore Mana Talauci -Minista

by Bello Hamza
2 years ago
Nijeriya

Bai kamata Nijeriya ta kasance tana fama da talauci ba, bayan tana zaune a kan dimbin ma’adanai shinfide a sassan kasar nan.

Ministan Ma’adanai, Dakta Dele Alake ya bayyana haka a taron baye kolin ma’adanai da kuma bayar da takardar shaida ga daliban da suka horo a kan sarrfa ma’adanai da kamfanin MinDiber ta dauki nauyi gabatarwa wanda aka gudanar a Abuja ranar Alhamis da ta gabata.

  • Gwamnatin Kwara Ta Tasa Keyar Mabarata 158 Zuwa Jihohinsu Na Asali
  • Matsalolin Tsaro Da Ambaliya: ‘Yan Nijeriya Sun Sayo Abinci Daga Waje Na Tiriliyan 3 – CBN

Dakta Alake ya kuma ce, kawo shirin kera sarkar gwalagwalai tamkar kawo arziki cikin gida Nijeriya ne.

ADVERTISEMENT

Ministan ya kuma bayar da kayan fara aiki ga wadanda suka koyi yadda ake kera gwalagwalan, ya ce mu su yanzu da aka basu kayan aiki tamkar an samar musu da hanyar cin abinci ne domin bunkasa rayuwarsu, ya kuma bukaci su bayar da nasu gudummawr domin bunkasa sashin hakar ma’adanai domin samun nasarar kasa gaba daya.

Ya kuma ce, “Babu wata jiha a kasar nan da ba ta da wani nau’in ma’adani da Allah ya shinfida a jihar, “a kan haka ban ga dalilimu na fama da talauci ba” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

“Indan da mun yi abin da ya kamata a shekarun baya, inda mun mayar da hankalinmu zuwa bangaren ma’adanai, da bangaren ya isa ya rike mana tattalin arziki. Amma sai muka ki saboda muna ganin an samu man fetur sai muka kulle idonmu daga abubuwa kamar gemstone, gwalagwalai da abin da ya shafi harkar gona.

Ya ce, a halin yanzu duniya tana nesa-nesa daga man fetur tana komawa abin da ya shafi wasu makamashi musamman ganin yadda fetur ke kara ta’azzarar karuwar dumamar yanayi.

A jawabinsa, shugaban kamfanin MinDiber, Injiniya Sallim Salaam ya ce, an shirya taron ne domin mika jinjina ga ‘yan Nijeriya da suka koya tare da kwarewa wajen kera gwala-gwalai, irin gwalagwalan da za su yi gogayya da irin wadanda ake kerawa a kashen duniya.
Ya ce, taron ya kuma zama fagen da wadanda suka samu horon za su baje kolin irin kayayyakin da suka kera domin duniya ta gani, ya kuma yaba da irin kokarin su a wannan fagen.

A kan haka ya kuma mika godiyarsa ga babban sakataren ma’aikatar ma’adanai a kan irin goyon bayan da suka samu wajen samun nasarar bikin baje kolin ya kuma yi alkawarin ci gaba da tallafa wa matasa don su bunkasa rayuwarsu.

Ya kuma nemi matasan da suka samu horon su koma jihohinsu domin su horars da wasu matasan, ta yadda suma za su samu abin dogaro da kai.

A nata jawabin, babbar sakatariyar ma’aikatar ma’adanai, Dakta Mary Ogbe, ta yi kira ne ga gwamnonin jihohi su tallafa wa matasan da kudaden da za su fadada harkokinsu tare da kuma horas da wasu matasan. Ta haka za a tabbatar da an hau hanyar yaki da talauci da zaman kashe wando a tsakanin matasan Nijeriya.

Taron ya samu halartar manyan ma’aikatan gwamnati, masu ruwa da tsaki a bangaren ma’adanai da sauran al’umma, inda suka yaba da irin ayyukan da matasan suka gabatar.

Daga cikin matasa 96 da suka fara horon matasa 36 ne suka samu nasarar kammala horon. Daya daga cikin matasan mai suna Felicitas Ella daga Jihar Kros Ribas ta mika godiyarta ga kamfanin da ya dauki nauyin horars da su ta kuma yi alkawarin aiki da abin da ta koya yadda kamata ta kuma yi alkawarin horas da wasu matasan a jihar su.

Minista
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Gwamnan Kano Ya Bada Umarnin Kamo Tsohon Sarkin Kano Aminu Ado Bayero

Gwamnan Kano Ya Bada Umarnin Kamo Tsohon Sarkin Kano Aminu Ado Bayero

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.