ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dimbin Ma’adinan Kasar Nan Sun Isa Su Kore Mana Talauci -Minista

by Bello Hamza
2 years ago
Nijeriya

Bai kamata Nijeriya ta kasance tana fama da talauci ba, bayan tana zaune a kan dimbin ma’adanai shinfide a sassan kasar nan.

Ministan Ma’adanai, Dakta Dele Alake ya bayyana haka a taron baye kolin ma’adanai da kuma bayar da takardar shaida ga daliban da suka horo a kan sarrfa ma’adanai da kamfanin MinDiber ta dauki nauyi gabatarwa wanda aka gudanar a Abuja ranar Alhamis da ta gabata.

  • Gwamnatin Kwara Ta Tasa Keyar Mabarata 158 Zuwa Jihohinsu Na Asali
  • Matsalolin Tsaro Da Ambaliya: ‘Yan Nijeriya Sun Sayo Abinci Daga Waje Na Tiriliyan 3 – CBN

Dakta Alake ya kuma ce, kawo shirin kera sarkar gwalagwalai tamkar kawo arziki cikin gida Nijeriya ne.

ADVERTISEMENT

Ministan ya kuma bayar da kayan fara aiki ga wadanda suka koyi yadda ake kera gwalagwalan, ya ce mu su yanzu da aka basu kayan aiki tamkar an samar musu da hanyar cin abinci ne domin bunkasa rayuwarsu, ya kuma bukaci su bayar da nasu gudummawr domin bunkasa sashin hakar ma’adanai domin samun nasarar kasa gaba daya.

Ya kuma ce, “Babu wata jiha a kasar nan da ba ta da wani nau’in ma’adani da Allah ya shinfida a jihar, “a kan haka ban ga dalilimu na fama da talauci ba” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Indan da mun yi abin da ya kamata a shekarun baya, inda mun mayar da hankalinmu zuwa bangaren ma’adanai, da bangaren ya isa ya rike mana tattalin arziki. Amma sai muka ki saboda muna ganin an samu man fetur sai muka kulle idonmu daga abubuwa kamar gemstone, gwalagwalai da abin da ya shafi harkar gona.

Ya ce, a halin yanzu duniya tana nesa-nesa daga man fetur tana komawa abin da ya shafi wasu makamashi musamman ganin yadda fetur ke kara ta’azzarar karuwar dumamar yanayi.

A jawabinsa, shugaban kamfanin MinDiber, Injiniya Sallim Salaam ya ce, an shirya taron ne domin mika jinjina ga ‘yan Nijeriya da suka koya tare da kwarewa wajen kera gwala-gwalai, irin gwalagwalan da za su yi gogayya da irin wadanda ake kerawa a kashen duniya.
Ya ce, taron ya kuma zama fagen da wadanda suka samu horon za su baje kolin irin kayayyakin da suka kera domin duniya ta gani, ya kuma yaba da irin kokarin su a wannan fagen.

A kan haka ya kuma mika godiyarsa ga babban sakataren ma’aikatar ma’adanai a kan irin goyon bayan da suka samu wajen samun nasarar bikin baje kolin ya kuma yi alkawarin ci gaba da tallafa wa matasa don su bunkasa rayuwarsu.

Ya kuma nemi matasan da suka samu horon su koma jihohinsu domin su horars da wasu matasan, ta yadda suma za su samu abin dogaro da kai.

A nata jawabin, babbar sakatariyar ma’aikatar ma’adanai, Dakta Mary Ogbe, ta yi kira ne ga gwamnonin jihohi su tallafa wa matasan da kudaden da za su fadada harkokinsu tare da kuma horas da wasu matasan. Ta haka za a tabbatar da an hau hanyar yaki da talauci da zaman kashe wando a tsakanin matasan Nijeriya.

Taron ya samu halartar manyan ma’aikatan gwamnati, masu ruwa da tsaki a bangaren ma’adanai da sauran al’umma, inda suka yaba da irin ayyukan da matasan suka gabatar.

Daga cikin matasa 96 da suka fara horon matasa 36 ne suka samu nasarar kammala horon. Daya daga cikin matasan mai suna Felicitas Ella daga Jihar Kros Ribas ta mika godiyarta ga kamfanin da ya dauki nauyin horars da su ta kuma yi alkawarin aiki da abin da ta koya yadda kamata ta kuma yi alkawarin horas da wasu matasan a jihar su.

Minista
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Gwamnan Kano Ya Bada Umarnin Kamo Tsohon Sarkin Kano Aminu Ado Bayero

Gwamnan Kano Ya Bada Umarnin Kamo Tsohon Sarkin Kano Aminu Ado Bayero

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.