ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Diphtheria: Kano Ce Kan Gaba A Yawan Masu Dauke Da Cutar Mashaƙo A Nijeriya

by Muhammad
2 years ago
Diphtheria

Hukumar NCDC mai yaki da cutuka masu yaduwa a Nijeriya ta ce cutar mashako (diphtheria) ta kashe mutum 80 a kasar daga watan Mayu zuwa Yunin bana.

BBC ta rawaito cewa, wani rahoton da hukumar ta fitar ta ce yanzu mutum 836 suka harbu da cutar kuma jihar Kano ce ta fi yawan wadanda suka kamu da ke da mutum 819.

  • Diphtheria: Mutane 123 Sun Kamu, 38 Sun Mutu A Jihohi 4 – NCDC
  • Diphtheria: Mutum 3 Sun Rasu, An Kwantar Da 7 A Asibiti A Kaduna

Hukumar ta ce alkaluman sun shafi kananan hukumomi 33 na jihohi bakwai da suka hada da Yobe da Katsina da Sokoto Zamfara da Kaduna da kuma Abuja.

ADVERTISEMENT

Ko a makon nan an bayar da rahoton mutuwar yara kusan 10 sakamakon cutar a jihar Kaduna.

”Ana cikin babban tashin hankali”

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

Tsohon shugaban hukumar yaki da cutuka masu yaduwa ta Nijeriyar Farfesa Abdussalam Nasidi, ya shaida wa BBC Hausa cewa halin da aka tsinci kai a ciki abun tashin hankali ne, ba na wasa ba.

Ya ce dole ne a tashi a dauki mataki, idan kuwa ba haka ba za a ji kunya.

”Ina mamaki kwarai, tunda bai kamata a ce ana yi wa yara rigakafin wannan cuta tun farko amma kuma ana samunta ba, abun ma da muke gani da ke tabbatar mana da cewa an gaza ne wajen yin rigakafin ko kuma wasu ba sa kai ‘ya’yansu a musu rigakafin shi ne kaso 80 ba a musu rigakafin ba.”

Ya ce wannan babbar gazawa ce da ke nuna ya kamata gwamnati da hukumomi su tashi su yi wa kansu kiyamallaili.

Farfesa Abdussalam Nasidi, ya kara da cewa a halin da ake ciki, idan har mutum ya kamu da cutar to ba lallai ne rigakafin ya yi aiki a kansa ba, ballantana da a yanzu haka ana fama da karancin rigakafin shi kansa.

Yadda cutar ke kama mutum

Masanin ya bayyana wa BBC cewa cutar mashakon, na kama makogaro ne, ta hana mutum sakat.

Ya ce: ”Idan ta kama mutum za ta rike masa wuya kamar an shake ka, idan ta kama yaro idan ba Allah ne Ya kiyaye ba a gaban iyayensa za a rasa shi, don haka babban barazana ce”

Likitoci sun ce hanya daya ta kauce wa kamuwa da cutar mashako ga manya da kananan yara ita ce yin allura saboda za ta kashe kwayoyin cutar da ke jikin mutum.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 
Manyan Labarai

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Next Post
Manhajar ‘Threads’ Da Yadda Ake Amfani Da Ita

Manhajar 'Threads' Da Yadda Ake Amfani Da Ita

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.