• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dokar Hana Sayar Da Burodi Mara Shaida, Litar Mai Fiye Da 50 Ta Tabbata A Zamfara, Gwamna Dauda Ya Sa Hannu

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai, Manyan Labarai
0
Dokar Hana Sayar Da Burodi Mara Shaida, Litar Mai Fiye Da 50 Ta Tabbata A Zamfara, Gwamna Dauda Ya Sa Hannu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal ya sanya hannu a kan dokar da ta haramta sayar da burodin da ba a liƙa takardar shaidar inda ake yin sa ba, tare da jigilar sa a buhu.

Haka kuma an haramta sayar da man fetur fiye da lita 50, haka ma an haramta motoci masu gilashi mai duhu a duk faɗin jihar Zamfara.

Sojoji Sun Ceto Mutane 10 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Zamfara

Dokar Hana Sayar Da Burodi Mara Shaida, Litar Mai Fiye Da 50 Ta Tabbata A Zamfara, Gwamna Dauda Ya Sa Hannu

A cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu, ta ce dokar mai lamba 02 da mai lamba ta 04, 2024 za ta taimaka wajen magance wasu matsalolin da ke taimakawa ga matsalar tsaro a jihar. Jiya Talata ne Gwamnan ya sanya hannu a dokar a gidan gwamnatin jihar da Gusau

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Kakain Gwamnan ya ce, an sanya dokar ne sakamakon hare-haren da ake kai wa wasu al’ummomi a sassan jihar.

“Sakamakon hare-haren da aka kai wa al’ummomin wasu Ƙananan Hukumomin jihar nan, musamman Zurmi, Shinkafi, Ƙaura Namoda da Talata Mafara, tare da samun ƙaruwar kai hare-hare da sace mutane a wasu yankuna da manyan hanyoyin jihar.

“Gwamna Lawal ya sanya hannu a dokar No. 02 2024, wacce ta haramta sayar da biredi mara takardar shaida, tare da sanya biredin a buhuna, an kuma haramta wasu ayyukan da ba a amince da su ba a jihar.

“Wajibi ne duk gidajen biredi su sanya takarda mai ɗauke da cikakken adireshin kamfanin, tare da bayanan ayyukan da su ke aiwatarwa, ana so su yi wannan cikin gaggawa.

“Kada wani gidan man fetur ya kuskura ya sayar da fiye da lita 50 ga kowace mota a lokaci guda. Daga yanzu kuma, gidajen mai za su sayar da mai ne tsakanin ƙarfe 6 na safe zuwa 6 na yamma.

“Sayarwa ko yawo da biredi, yanzu zai zama kawai a Hedikwatar kowace Ƙaramar Hukuma: Amma a Gusau, an amince a sayar a yankunan: Hanyar Damba—Zaria; Gada Biyu—Sokoto; Command Guest House a hanyar Ƙaura Namoda; Gusau Garage—Dansadau.”

Haka kuma dokar ta No. 04, 2024, wacce Gwamnan ya sanya wa hannu, ta haramta motoci masu ɗauke da gilashi mai duhu a Zamfara. “Haka kuma an haramta wa masu motoci rufe lambar motocin su a yayin da suke tafiya.

“Wajibi ne duk masu motoci su kasance tare da cikakkun takardunsu, sannan su bi dokar kiyaye dokokin hanya ta jihar Zamfara mai lamba No. 2, 2015, ko duk wata doka da ta shafi wannan.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 50BurodiFeturGwamna Dauda LawalLitaMaiTsaroZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Next Post

Kamfanin Huawei Ya Horas Da Matasa 241 A Arewacin Uganda

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

3 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

6 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

6 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

16 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

18 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

19 hours ago
Next Post
Kamfanin Huawei Ya Horas Da Matasa 241 A Arewacin Uganda

Kamfanin Huawei Ya Horas Da Matasa 241 A Arewacin Uganda

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.