ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dokar Kayyade Tsadar Aure Ta Samu Karatu Na Biyu A Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
Aure

Dokar kayyade tsadar bukukuwan aure, zanen suna, kaciya da makamantansu a Sakkwato ta tsallake karatu na biyu a Majalisar Dokokin Jihar.

Wannan ya biyo bayan gabatar da kudurin dokar da Honarabul Abubakar Shehu Shamaki (APC- Yabo) ya gabatar tare da gudunmuwar Honarabul Faruku Balle (PDP- Gudu) a zaman Majalisar Dokokin a yau.

  • An Bude Bikin Anime Na Kasa Da Kasa Karo Na 18 A Hangzhou
  • Yadda ISWAP Ta Kai Hari Sansanin Sojoji, Mutane Da Dama Sun Mutu A Jihar Borno

Da yake gabatar da dokar, Honarabul Shamaki, ya bayyana cewar dokar na da manufar kayyade da takaitawa daidai gwargwado kan tsada da sharholiya da ake yi a bukukuwan aure, zanen suna da kaciya a Sakkwato.

ADVERTISEMENT

Ya ce ko shakka babu dabi’ar almubazzaranci da ake yi da sunan bukukuwa ba karamar illa ba ce wadda ke haifar da tabarbarewar tattalin arziki a cikin al’umma.

“Wannan bakar dabi’ar idan aka ci gaba a haka ba tare da daukar mataki da kayyadewa ba, za ta sa aure ya yi wa jama’a matukar wahala wanda hakan zai iya haifar da zina, madugo, luwadi da sauran ayyukan assha,” In ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Dan majalisar ya kara da cewar a yanzu haka kasawar ango ga yin hidimar da aka bukata da sharholiya a yayin aure na haifar da watsewar auren baki daya.

“Matsalar ta haifar da yawaitar mace-macen aure a cikin al’umma. Don haka idan wannan dokar ta tsallake aka sa mata hannu a matsayin doka, za ta taimaka kwarai wajen rage tsadar aure da sharholiyar da ake yi da takaita yawan zawarawa,” ya bayyana.

A kan wannan Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Sakkwato, Honarabul Aminu Achida, ya bukaci jin ra’ayin ‘yan majalisar wadanda baki daya su 30 suka aminta da karatu na biyu na dokar wanda a bisa ga wannan ya tura kudurin dokar a gaban kwamitin majalisa kan Harkokin Addini domin daukar matakin doka na gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
Nazari

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Next Post
Yaushe Ne Za A Ga Bayan Hare-haren Bindiga A Kasar Amurka?

Yaushe Ne Za A Ga Bayan Hare-haren Bindiga A Kasar Amurka?

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.