• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Rahotonni
0
Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Gamayyar Kungiyoyin Masatan Arewa Mazauna Legas, Alhaji Ibrahim Galadanci ya bayyana cewa dole ne gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele ya gurfana a gaban kuliya.

Shugaban gamayyar ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da manema labarai a makon nan.
Ya ce zargin da ake yi wa gwamnan CBN ya yi yawa kuma a matsayinsa na babban mutum da yake rike da ofis mai daraja a Nijeriya, domin ana zarginsa da almundahana da raba kudade ga ‘yan ta’adda da kuma rarraba kudade ba bisa ka’ida ba, bisa haka ne yake ganin ya kamata ya gurfana a gaban kotu saboda ya wanke kansa daga wadannan zarge-zarge idan har yana da gaskiya, idan kuma aka same shi da laifi a hukunta shi daidai da laifinsa.

A cewarsa, babu wanda ya fi karfin doka a Nijeriya, duk wanda ya karya doka idan har akwai adalci a gurfanar da shi a gaban kotu.

Ya kara da cewa akwai alamun kamshin gaskiya cikin wadannan zarge-zarge tun da majalisa ta kira shi ya ki zuwa, sannan Sanata Gudaji Kazaure ya fito karara ya fadi abubuwa a kansa kuma ya kamata a yi bincike a kan lamarin, idan har yana da hujjoji ba zai taba yarda wadannan maganganun su yi tasiri a kansa ba.

Alhaji Ibrahim ya ce hakki ne na shugaban kasa wanda ya nada Emefiele kan wannan mukami ya kafa alkalai da za su gudanar da bincike kan wannan zarge-zarge da ake yi masa.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Ya ce ya kamata shugaban kasa ya shiga cikin wannan zance gadan-gadan domin warware zare da abawa idan har yana son ceto Nijeriya, saboda kar ya tafi ya bar kasar da kura a kasa. Ya jaddada cewa wannan ba karamin lamari ba ne wanda ya kamata shugaban kasa ya yi rawar gani kan abubuwan da aka binciko kan lamari.

Shugaban matasan ya ce shugaban kasa a matsayinsa na adali uban kowa da kowa ne da ke kasar nan, ya kamata ya dauki mataki kan wannan zargi, domin mafi yawancin alkalan Nijeriya fuska biyu suke da shi, wanda shugaban kasa ya san da haka, ya kamata shugaban kasa ya kafa kwamitinsa wanda shi kadai za a bai wa sakamakon rahoton da aka bankado.

Ya ce kamar yadda ya rage saura kwanaki kalilan shugaban kasa ya bar karagar mulki, ya kamata ya san wani irin mataki zai dauka domin ya wanke kansa. Ya ce maganar ko kadan ba ta siyasa ba ce, akwai marasa kishin kasa shafaffu da mai masu yin amfani da kujeransu wajen lalata kasa a cikin gwamnatin nan.

Alhaji Ibrahim ya ce rawar da za su iya takawa a kungiyance shi ne, ci gaba da kiraye-kiraye har ya kai ga hunnun shugaban kasa domin ya dauki matakan da suka dace, saboda shi Allah ya bai wa amanar wannan kasa kuma zai tambaye shi yadda ya gudanar da shugabancinsa.

Ya ce mafi yawancin ‘yan Nijeriya na cikin wahala, tsirarun mutane ne suke jin dadi a kasar nan, kuma wannan ba karamin zargi ba ne wanda gwamnati za ta iya yin burus da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Shirya Tsaf Za Mu Kori Jami’yyar APC Daga Mulkin Katsina Har Da Nijeriya – Nura Khalil

Next Post

Addini: Shin Saudiyya Zata Iya Hukunta Ronaldo?

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

2 days ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

6 days ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

1 week ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

1 week ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

2 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

2 weeks ago
Next Post
Addini: Shin Saudiyya Zata Iya Hukunta Ronaldo?

Addini: Shin Saudiyya Zata Iya Hukunta Ronaldo?

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.