• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Rahotonni
0
Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Gamayyar Kungiyoyin Masatan Arewa Mazauna Legas, Alhaji Ibrahim Galadanci ya bayyana cewa dole ne gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele ya gurfana a gaban kuliya.

Shugaban gamayyar ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da manema labarai a makon nan.
Ya ce zargin da ake yi wa gwamnan CBN ya yi yawa kuma a matsayinsa na babban mutum da yake rike da ofis mai daraja a Nijeriya, domin ana zarginsa da almundahana da raba kudade ga ‘yan ta’adda da kuma rarraba kudade ba bisa ka’ida ba, bisa haka ne yake ganin ya kamata ya gurfana a gaban kotu saboda ya wanke kansa daga wadannan zarge-zarge idan har yana da gaskiya, idan kuma aka same shi da laifi a hukunta shi daidai da laifinsa.

A cewarsa, babu wanda ya fi karfin doka a Nijeriya, duk wanda ya karya doka idan har akwai adalci a gurfanar da shi a gaban kotu.

Ya kara da cewa akwai alamun kamshin gaskiya cikin wadannan zarge-zarge tun da majalisa ta kira shi ya ki zuwa, sannan Sanata Gudaji Kazaure ya fito karara ya fadi abubuwa a kansa kuma ya kamata a yi bincike a kan lamarin, idan har yana da hujjoji ba zai taba yarda wadannan maganganun su yi tasiri a kansa ba.

Alhaji Ibrahim ya ce hakki ne na shugaban kasa wanda ya nada Emefiele kan wannan mukami ya kafa alkalai da za su gudanar da bincike kan wannan zarge-zarge da ake yi masa.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Ya ce ya kamata shugaban kasa ya shiga cikin wannan zance gadan-gadan domin warware zare da abawa idan har yana son ceto Nijeriya, saboda kar ya tafi ya bar kasar da kura a kasa. Ya jaddada cewa wannan ba karamin lamari ba ne wanda ya kamata shugaban kasa ya yi rawar gani kan abubuwan da aka binciko kan lamari.

Shugaban matasan ya ce shugaban kasa a matsayinsa na adali uban kowa da kowa ne da ke kasar nan, ya kamata ya dauki mataki kan wannan zargi, domin mafi yawancin alkalan Nijeriya fuska biyu suke da shi, wanda shugaban kasa ya san da haka, ya kamata shugaban kasa ya kafa kwamitinsa wanda shi kadai za a bai wa sakamakon rahoton da aka bankado.

Ya ce kamar yadda ya rage saura kwanaki kalilan shugaban kasa ya bar karagar mulki, ya kamata ya san wani irin mataki zai dauka domin ya wanke kansa. Ya ce maganar ko kadan ba ta siyasa ba ce, akwai marasa kishin kasa shafaffu da mai masu yin amfani da kujeransu wajen lalata kasa a cikin gwamnatin nan.

Alhaji Ibrahim ya ce rawar da za su iya takawa a kungiyance shi ne, ci gaba da kiraye-kiraye har ya kai ga hunnun shugaban kasa domin ya dauki matakan da suka dace, saboda shi Allah ya bai wa amanar wannan kasa kuma zai tambaye shi yadda ya gudanar da shugabancinsa.

Ya ce mafi yawancin ‘yan Nijeriya na cikin wahala, tsirarun mutane ne suke jin dadi a kasar nan, kuma wannan ba karamin zargi ba ne wanda gwamnati za ta iya yin burus da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Shirya Tsaf Za Mu Kori Jami’yyar APC Daga Mulkin Katsina Har Da Nijeriya – Nura Khalil

Next Post

Addini: Shin Saudiyya Zata Iya Hukunta Ronaldo?

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
CBN
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

3 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

4 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

4 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Addini: Shin Saudiyya Zata Iya Hukunta Ronaldo?

Addini: Shin Saudiyya Zata Iya Hukunta Ronaldo?

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.