• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Rahotonni
0
Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Gamayyar Kungiyoyin Masatan Arewa Mazauna Legas, Alhaji Ibrahim Galadanci ya bayyana cewa dole ne gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele ya gurfana a gaban kuliya.

Shugaban gamayyar ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da manema labarai a makon nan.
Ya ce zargin da ake yi wa gwamnan CBN ya yi yawa kuma a matsayinsa na babban mutum da yake rike da ofis mai daraja a Nijeriya, domin ana zarginsa da almundahana da raba kudade ga ‘yan ta’adda da kuma rarraba kudade ba bisa ka’ida ba, bisa haka ne yake ganin ya kamata ya gurfana a gaban kotu saboda ya wanke kansa daga wadannan zarge-zarge idan har yana da gaskiya, idan kuma aka same shi da laifi a hukunta shi daidai da laifinsa.

A cewarsa, babu wanda ya fi karfin doka a Nijeriya, duk wanda ya karya doka idan har akwai adalci a gurfanar da shi a gaban kotu.

Ya kara da cewa akwai alamun kamshin gaskiya cikin wadannan zarge-zarge tun da majalisa ta kira shi ya ki zuwa, sannan Sanata Gudaji Kazaure ya fito karara ya fadi abubuwa a kansa kuma ya kamata a yi bincike a kan lamarin, idan har yana da hujjoji ba zai taba yarda wadannan maganganun su yi tasiri a kansa ba.

Alhaji Ibrahim ya ce hakki ne na shugaban kasa wanda ya nada Emefiele kan wannan mukami ya kafa alkalai da za su gudanar da bincike kan wannan zarge-zarge da ake yi masa.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Ya ce ya kamata shugaban kasa ya shiga cikin wannan zance gadan-gadan domin warware zare da abawa idan har yana son ceto Nijeriya, saboda kar ya tafi ya bar kasar da kura a kasa. Ya jaddada cewa wannan ba karamin lamari ba ne wanda ya kamata shugaban kasa ya yi rawar gani kan abubuwan da aka binciko kan lamari.

Shugaban matasan ya ce shugaban kasa a matsayinsa na adali uban kowa da kowa ne da ke kasar nan, ya kamata ya dauki mataki kan wannan zargi, domin mafi yawancin alkalan Nijeriya fuska biyu suke da shi, wanda shugaban kasa ya san da haka, ya kamata shugaban kasa ya kafa kwamitinsa wanda shi kadai za a bai wa sakamakon rahoton da aka bankado.

Ya ce kamar yadda ya rage saura kwanaki kalilan shugaban kasa ya bar karagar mulki, ya kamata ya san wani irin mataki zai dauka domin ya wanke kansa. Ya ce maganar ko kadan ba ta siyasa ba ce, akwai marasa kishin kasa shafaffu da mai masu yin amfani da kujeransu wajen lalata kasa a cikin gwamnatin nan.

Alhaji Ibrahim ya ce rawar da za su iya takawa a kungiyance shi ne, ci gaba da kiraye-kiraye har ya kai ga hunnun shugaban kasa domin ya dauki matakan da suka dace, saboda shi Allah ya bai wa amanar wannan kasa kuma zai tambaye shi yadda ya gudanar da shugabancinsa.

Ya ce mafi yawancin ‘yan Nijeriya na cikin wahala, tsirarun mutane ne suke jin dadi a kasar nan, kuma wannan ba karamin zargi ba ne wanda gwamnati za ta iya yin burus da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Shirya Tsaf Za Mu Kori Jami’yyar APC Daga Mulkin Katsina Har Da Nijeriya – Nura Khalil

Next Post

Addini: Shin Saudiyya Zata Iya Hukunta Ronaldo?

Related

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

1 day ago
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

1 day ago
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

2 days ago
Yadda Sanata Barau Ke Samar da Masana Don Ci Gaban Kano
Rahotonni

Yadda Sanata Barau Ke Samar da Masana Don Ci Gaban Kano

2 days ago
Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu
Rahotonni

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

1 week ago
Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba
Rahotonni

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

1 week ago
Next Post
Addini: Shin Saudiyya Zata Iya Hukunta Ronaldo?

Addini: Shin Saudiyya Zata Iya Hukunta Ronaldo?

LABARAI MASU NASABA

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

October 5, 2025
Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

October 5, 2025
Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.