• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Rahotonni
0
Dole Gwamnan CBN Ya Gurfana A Gaban Kuliya – Alhaji Ibrahim
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Gamayyar Kungiyoyin Masatan Arewa Mazauna Legas, Alhaji Ibrahim Galadanci ya bayyana cewa dole ne gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele ya gurfana a gaban kuliya.

Shugaban gamayyar ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da manema labarai a makon nan.
Ya ce zargin da ake yi wa gwamnan CBN ya yi yawa kuma a matsayinsa na babban mutum da yake rike da ofis mai daraja a Nijeriya, domin ana zarginsa da almundahana da raba kudade ga ‘yan ta’adda da kuma rarraba kudade ba bisa ka’ida ba, bisa haka ne yake ganin ya kamata ya gurfana a gaban kotu saboda ya wanke kansa daga wadannan zarge-zarge idan har yana da gaskiya, idan kuma aka same shi da laifi a hukunta shi daidai da laifinsa.

A cewarsa, babu wanda ya fi karfin doka a Nijeriya, duk wanda ya karya doka idan har akwai adalci a gurfanar da shi a gaban kotu.

Ya kara da cewa akwai alamun kamshin gaskiya cikin wadannan zarge-zarge tun da majalisa ta kira shi ya ki zuwa, sannan Sanata Gudaji Kazaure ya fito karara ya fadi abubuwa a kansa kuma ya kamata a yi bincike a kan lamarin, idan har yana da hujjoji ba zai taba yarda wadannan maganganun su yi tasiri a kansa ba.

Alhaji Ibrahim ya ce hakki ne na shugaban kasa wanda ya nada Emefiele kan wannan mukami ya kafa alkalai da za su gudanar da bincike kan wannan zarge-zarge da ake yi masa.

Labarai Masu Nasaba

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

Ya ce ya kamata shugaban kasa ya shiga cikin wannan zance gadan-gadan domin warware zare da abawa idan har yana son ceto Nijeriya, saboda kar ya tafi ya bar kasar da kura a kasa. Ya jaddada cewa wannan ba karamin lamari ba ne wanda ya kamata shugaban kasa ya yi rawar gani kan abubuwan da aka binciko kan lamari.

Shugaban matasan ya ce shugaban kasa a matsayinsa na adali uban kowa da kowa ne da ke kasar nan, ya kamata ya dauki mataki kan wannan zargi, domin mafi yawancin alkalan Nijeriya fuska biyu suke da shi, wanda shugaban kasa ya san da haka, ya kamata shugaban kasa ya kafa kwamitinsa wanda shi kadai za a bai wa sakamakon rahoton da aka bankado.

Ya ce kamar yadda ya rage saura kwanaki kalilan shugaban kasa ya bar karagar mulki, ya kamata ya san wani irin mataki zai dauka domin ya wanke kansa. Ya ce maganar ko kadan ba ta siyasa ba ce, akwai marasa kishin kasa shafaffu da mai masu yin amfani da kujeransu wajen lalata kasa a cikin gwamnatin nan.

Alhaji Ibrahim ya ce rawar da za su iya takawa a kungiyance shi ne, ci gaba da kiraye-kiraye har ya kai ga hunnun shugaban kasa domin ya dauki matakan da suka dace, saboda shi Allah ya bai wa amanar wannan kasa kuma zai tambaye shi yadda ya gudanar da shugabancinsa.

Ya ce mafi yawancin ‘yan Nijeriya na cikin wahala, tsirarun mutane ne suke jin dadi a kasar nan, kuma wannan ba karamin zargi ba ne wanda gwamnati za ta iya yin burus da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Shirya Tsaf Za Mu Kori Jami’yyar APC Daga Mulkin Katsina Har Da Nijeriya – Nura Khalil

Next Post

Addini: Shin Saudiyya Zata Iya Hukunta Ronaldo?

Related

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

1 day ago
Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa
Rahotonni

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

1 week ago
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
Rahotonni

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

1 week ago
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

1 week ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

4 weeks ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

4 weeks ago
Next Post
Addini: Shin Saudiyya Zata Iya Hukunta Ronaldo?

Addini: Shin Saudiyya Zata Iya Hukunta Ronaldo?

LABARAI MASU NASABA

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.