• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Mu Yi Gaggawar Cire Tallafin Mai Ko Ya Halaka ‘Yan Nijeriya – Shettima

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Shettima

Mataimakin Shugaban kasa, Kashim Shettima, ya bayar da hujjar cewa akwai bukatar a kawo karshen tallafin man fetur a kasar nan, yana mai cewa idan har ba a yi gaggawar cire tallafi ba, to zai hakala ‘yan Nijeriya.

A cewarsa, sabuwar gwamnati ta yi hasashen cewa za a fuskanci adawa mai tsanani kan matakin da ta dauka na cire tallafin man fetur, amma ya lura cewa akwai bukatar dagewa wajen cimma wannan buri.

  • Tallafin Mai: Ba A Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da NLC Ba

Shettima ya bayyana hakan ne a ranar Talata lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar farko da ya hau kan karagar mulki a fadar gwamnati da ke Abuja, sai dai ya yi gargadin cewa Nijeriya na bukatar kawar da tallafin mai, idan ba haka ba tallafin zai kawar da al’ummar Nijeriya.

Ya jaddada cewa tsarin tallafin ba ya amfanar da talakan Nijeriya, sai dai yana tallafa wa rayuwar masu hannu da shuni. Ya tabbatar da cewa duk da adawar da ake sa ran masu cin gajiyar tsarin tallafin za su yi, Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu kasancewarsa mai kishin kasa zai magance barazanar da ake fuskanta a bangaren mai gaba daya.

“Tuni shugaban kasa ya yi sanarwa kan batun tallafin man fetur. Maganar gaskiya ita ce ko dai mu cire tallafi yanzu ko kuma tallafin man fetur ya kawar da al’ummar Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

“A shekarar 2022, mun kashe dala biliyan 10 wajen tallafa wa rayuwar masu hannu da shuni, saboda ni da ku ba ma amfana da kashi 90 daga tallafin man fetur. Talakawa kashi 40 cikin 100 na ’yan Nijeriya kadan ne ke amfana kuma hakan babbar illar ce.

“Za mu fuskanci adawa mai zafi daga wadanda ke cin gajiyar badakkalar tallafin man fetur, amma hakan shi ya fi dacewa. Ku tabbata cewa shugabanmu mutum ne mai kwarjini da kuma yakini..

“A cikar lokaci za ku yaba da kyawawan manufofinsa ga al’umma. Batun tallafin man fetur za a tunkari matsalar gaba daya. Da zarar mun yi haka, zai fi kyau,” in ji shi.

Da yake tsokaci kan batun canjin kudaden kasashen waje, mataimakin shugaban kasar ya ba da tabbacin cewa “za mu durkusar da kudaden waje gaba daya.

Ya kuma bayyana cewa nan ba da dadewa ba Shugaba Tinubu zai fito da ajandar sabuwar gwamnatin da za ta amfani daukacin ‘yan Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
TCN
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI
Labarai

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Next Post
Nijeriya

Samar Da Kyakkyawar Makoma Ga Yaran Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.