• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Mu Yi Gaggawar Cire Tallafin Mai Ko Ya Halaka ‘Yan Nijeriya – Shettima

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Shettima

Mataimakin Shugaban kasa, Kashim Shettima, ya bayar da hujjar cewa akwai bukatar a kawo karshen tallafin man fetur a kasar nan, yana mai cewa idan har ba a yi gaggawar cire tallafi ba, to zai hakala ‘yan Nijeriya.

A cewarsa, sabuwar gwamnati ta yi hasashen cewa za a fuskanci adawa mai tsanani kan matakin da ta dauka na cire tallafin man fetur, amma ya lura cewa akwai bukatar dagewa wajen cimma wannan buri.

  • Tallafin Mai: Ba A Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da NLC Ba

Shettima ya bayyana hakan ne a ranar Talata lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar farko da ya hau kan karagar mulki a fadar gwamnati da ke Abuja, sai dai ya yi gargadin cewa Nijeriya na bukatar kawar da tallafin mai, idan ba haka ba tallafin zai kawar da al’ummar Nijeriya.

Ya jaddada cewa tsarin tallafin ba ya amfanar da talakan Nijeriya, sai dai yana tallafa wa rayuwar masu hannu da shuni. Ya tabbatar da cewa duk da adawar da ake sa ran masu cin gajiyar tsarin tallafin za su yi, Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu kasancewarsa mai kishin kasa zai magance barazanar da ake fuskanta a bangaren mai gaba daya.

“Tuni shugaban kasa ya yi sanarwa kan batun tallafin man fetur. Maganar gaskiya ita ce ko dai mu cire tallafi yanzu ko kuma tallafin man fetur ya kawar da al’ummar Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i

“A shekarar 2022, mun kashe dala biliyan 10 wajen tallafa wa rayuwar masu hannu da shuni, saboda ni da ku ba ma amfana da kashi 90 daga tallafin man fetur. Talakawa kashi 40 cikin 100 na ’yan Nijeriya kadan ne ke amfana kuma hakan babbar illar ce.

“Za mu fuskanci adawa mai zafi daga wadanda ke cin gajiyar badakkalar tallafin man fetur, amma hakan shi ya fi dacewa. Ku tabbata cewa shugabanmu mutum ne mai kwarjini da kuma yakini..

“A cikar lokaci za ku yaba da kyawawan manufofinsa ga al’umma. Batun tallafin man fetur za a tunkari matsalar gaba daya. Da zarar mun yi haka, zai fi kyau,” in ji shi.

Da yake tsokaci kan batun canjin kudaden kasashen waje, mataimakin shugaban kasar ya ba da tabbacin cewa “za mu durkusar da kudaden waje gaba daya.

Ya kuma bayyana cewa nan ba da dadewa ba Shugaba Tinubu zai fito da ajandar sabuwar gwamnatin da za ta amfani daukacin ‘yan Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i
Labarai

JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i

October 18, 2025
An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba
Labarai

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

October 18, 2025
Next Post
Nijeriya

Samar Da Kyakkyawar Makoma Ga Yaran Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025
Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Zanta Da Sakataren Baitul-mali Da Wakilin Cinikayyar Amurka

Mataimakin Firaministan Sin Ya Zanta Da Sakataren Baitul-mali Da Wakilin Cinikayyar Amurka

October 18, 2025
JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i

JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.