• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Mu Yi Gaggawar Cire Tallafin Mai Ko Ya Halaka ‘Yan Nijeriya – Shettima

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Shettima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakin Shugaban kasa, Kashim Shettima, ya bayar da hujjar cewa akwai bukatar a kawo karshen tallafin man fetur a kasar nan, yana mai cewa idan har ba a yi gaggawar cire tallafi ba, to zai hakala ‘yan Nijeriya.

A cewarsa, sabuwar gwamnati ta yi hasashen cewa za a fuskanci adawa mai tsanani kan matakin da ta dauka na cire tallafin man fetur, amma ya lura cewa akwai bukatar dagewa wajen cimma wannan buri.

  • Tallafin Mai: Ba A Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da NLC Ba

Shettima ya bayyana hakan ne a ranar Talata lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar farko da ya hau kan karagar mulki a fadar gwamnati da ke Abuja, sai dai ya yi gargadin cewa Nijeriya na bukatar kawar da tallafin mai, idan ba haka ba tallafin zai kawar da al’ummar Nijeriya.

Ya jaddada cewa tsarin tallafin ba ya amfanar da talakan Nijeriya, sai dai yana tallafa wa rayuwar masu hannu da shuni. Ya tabbatar da cewa duk da adawar da ake sa ran masu cin gajiyar tsarin tallafin za su yi, Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu kasancewarsa mai kishin kasa zai magance barazanar da ake fuskanta a bangaren mai gaba daya.

“Tuni shugaban kasa ya yi sanarwa kan batun tallafin man fetur. Maganar gaskiya ita ce ko dai mu cire tallafi yanzu ko kuma tallafin man fetur ya kawar da al’ummar Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

“A shekarar 2022, mun kashe dala biliyan 10 wajen tallafa wa rayuwar masu hannu da shuni, saboda ni da ku ba ma amfana da kashi 90 daga tallafin man fetur. Talakawa kashi 40 cikin 100 na ’yan Nijeriya kadan ne ke amfana kuma hakan babbar illar ce.

“Za mu fuskanci adawa mai zafi daga wadanda ke cin gajiyar badakkalar tallafin man fetur, amma hakan shi ya fi dacewa. Ku tabbata cewa shugabanmu mutum ne mai kwarjini da kuma yakini..

“A cikar lokaci za ku yaba da kyawawan manufofinsa ga al’umma. Batun tallafin man fetur za a tunkari matsalar gaba daya. Da zarar mun yi haka, zai fi kyau,” in ji shi.

Da yake tsokaci kan batun canjin kudaden kasashen waje, mataimakin shugaban kasar ya ba da tabbacin cewa “za mu durkusar da kudaden waje gaba daya.

Ya kuma bayyana cewa nan ba da dadewa ba Shugaba Tinubu zai fito da ajandar sabuwar gwamnatin da za ta amfani daukacin ‘yan Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Nijeriya Na 16: Jan Aikin Da Ke Gaban Jagaban

Next Post

Samar Da Kyakkyawar Makoma Ga Yaran Nijeriya

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

5 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

6 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

7 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

7 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

8 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

8 hours ago
Next Post
Nijeriya

Samar Da Kyakkyawar Makoma Ga Yaran Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.