ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Mu Yi Gaggawar Cire Tallafin Mai Ko Ya Halaka ‘Yan Nijeriya – Shettima

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Shettima

Mataimakin Shugaban kasa, Kashim Shettima, ya bayar da hujjar cewa akwai bukatar a kawo karshen tallafin man fetur a kasar nan, yana mai cewa idan har ba a yi gaggawar cire tallafi ba, to zai hakala ‘yan Nijeriya.

A cewarsa, sabuwar gwamnati ta yi hasashen cewa za a fuskanci adawa mai tsanani kan matakin da ta dauka na cire tallafin man fetur, amma ya lura cewa akwai bukatar dagewa wajen cimma wannan buri.

  • Tallafin Mai: Ba A Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da NLC Ba

Shettima ya bayyana hakan ne a ranar Talata lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar farko da ya hau kan karagar mulki a fadar gwamnati da ke Abuja, sai dai ya yi gargadin cewa Nijeriya na bukatar kawar da tallafin mai, idan ba haka ba tallafin zai kawar da al’ummar Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Ya jaddada cewa tsarin tallafin ba ya amfanar da talakan Nijeriya, sai dai yana tallafa wa rayuwar masu hannu da shuni. Ya tabbatar da cewa duk da adawar da ake sa ran masu cin gajiyar tsarin tallafin za su yi, Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu kasancewarsa mai kishin kasa zai magance barazanar da ake fuskanta a bangaren mai gaba daya.

“Tuni shugaban kasa ya yi sanarwa kan batun tallafin man fetur. Maganar gaskiya ita ce ko dai mu cire tallafi yanzu ko kuma tallafin man fetur ya kawar da al’ummar Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

“A shekarar 2022, mun kashe dala biliyan 10 wajen tallafa wa rayuwar masu hannu da shuni, saboda ni da ku ba ma amfana da kashi 90 daga tallafin man fetur. Talakawa kashi 40 cikin 100 na ’yan Nijeriya kadan ne ke amfana kuma hakan babbar illar ce.

“Za mu fuskanci adawa mai zafi daga wadanda ke cin gajiyar badakkalar tallafin man fetur, amma hakan shi ya fi dacewa. Ku tabbata cewa shugabanmu mutum ne mai kwarjini da kuma yakini..

“A cikar lokaci za ku yaba da kyawawan manufofinsa ga al’umma. Batun tallafin man fetur za a tunkari matsalar gaba daya. Da zarar mun yi haka, zai fi kyau,” in ji shi.

Da yake tsokaci kan batun canjin kudaden kasashen waje, mataimakin shugaban kasar ya ba da tabbacin cewa “za mu durkusar da kudaden waje gaba daya.

Ya kuma bayyana cewa nan ba da dadewa ba Shugaba Tinubu zai fito da ajandar sabuwar gwamnatin da za ta amfani daukacin ‘yan Nijeriya.

Shettima
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Nijeriya

Samar Da Kyakkyawar Makoma Ga Yaran Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.