• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Ne A Tauna Tsakuwa Don Aya Ta Ji Tsoro

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Tsakuwa

Rundunar ‘yantar da jama’ar kasar Sin (PLA) ta yankin gabashin kasar ta shirya sojojinta na kasa, da na ruwa, da na sama da na harba makamai masu linzami, domin gudanar da atisaye mai taken “Joint Sword-2024B” a mashigin tekun Taiwan da arewa, da kudu da gabashin yankin tsibirin Taiwan.

 

Da farko dai, Taiwan wani yanki ne na kasar Sin da babban yankin ya sha nanata cewa ba zai iya ballewa ba, kuma dukkan wasu batutuwa da suka shafi tsibirin, batu ne na cikin gidan Sin. Amma wasu aikace aikace da bangarori masu adawa da dunkulewar baki dayan Sin wuri guda suke yi, wani yunkuri ne na takalar kasar Sin da keta cikakken ikon da take da shi kan yankunanta.

  • Ko Za A Kore Ni Daga APC Ba Zan Daina Fadar Gaskiya Ba – Ndume
  • Zaɓen Ƙananan Hukumomi: Mataimakiyar Gwamna Ta Yi Kira A Guji Tarzoma A Rungumi Zaman Lafiya

Babu wata kasa a duniya da za ta amince da irin takalar da ake yi wa kasar Sin don gane da batun Taiwan, don haka, matakan da Sin ke dauka sun zama wajibi domin bangarori masu ruwa da tsaki su farga, kuma su gane cewa Sin ba za ta nade hannu tana kallo ana keta cikakken ikon da ‘yanci da muradunta ba.

 

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Abin takaici ne yadda wasu ke nanata girmama manufar Sin daya tak, amma kuma suke nuna fuska biyu ta hanyar goyon bayan ‘yan awaren Taiwan, wanda kuma abu ne da Sin ba za ta lamunta ba.

 

‘Yancin Taiwan na nufin tashin hankali a Taiwan. Ya kamata mahukuntan yankin Taiwan da suke ganin suna samun goyon bayan wata babbar kasa, su nutsu, su yi nazarin yankuna irin nasu da aka yi ta ingizawa su nemi ‘yanci, shin yanzu a wani hali ko yanayi suke ciki? Duk wanda ke kaunar ci gaba da zaman lafiya da kwanciyar hankalin yankin, to ba zai goyi bayan ‘yancin Taiwan ba, sai dai idan yana da wata manufa da ta sabawa hakan.

 

Don haka, tilas ne Sin ta rika tauna tsakuwa don aya ta ji tsoro, kuma ‘yan awaren da masu ingizasu su san cewa, ba za ta yi kasa a gwiwa wajen daukan dukkan matakai domin kare cikakken ‘yanci da muradunta da burinta ba, wato ganin dunkulewar kasar wuri guda.(Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Next Post
An Yi Musayar Yawu Tsakanin Macron Da Netanyahu Kan Rikicin Gabas ta Tsakiya

An Yi Musayar Yawu Tsakanin Macron Da Netanyahu Kan Rikicin Gabas ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.