• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Ne Mu Ajiye Bambancin Addini, Ƙabilanci Da Siyasa A Baya – Ministan Yaɗa Labarai

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Dole Ne Mu Ajiye Bambancin Addini, Ƙabilanci Da Siyasa A Baya – Ministan Yaɗa Labarai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata tabbatacciyar hanya ta samun haɗin kan ‘yan kasa, itace sanya bambancin ƙabilanci, addini, da siyasa a baya, hakan zai samar da ƙarfafa amana da amincewa a tsakanin ‘yan Nijeriya.

Mataimaki na Musamman kan Yaɗa Labarai ga ministan yada labarai, Malam Rabi’u Ibrahim ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai, inda ya ce, Minista Muhammad Idris ya bayyana muhimmancin sanya banbancin dake tsakanin ‘yan kasa a baya domin samun nagartacciyar kasa a yayin da yake jawabi a taron farko na masu magana da yawu wanda Cibiyar Hulɗa Da Jama’a ta Nijeriya (NIPR) ta shirya tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai ta Tarayya a ranar Talata a Abuja.

  • Sojoji Sun Wanke Fursunoni 200 Da Ake Zargin Alaka Da Boko Haram A Borno
  • Masu Satar Mutane Za Mu Dauke Su A Matsayin ‘Yan Ta’adda – Tinubu

Da yake jawabi kan taken taron, wato “Canza Labari, Canza Al’umma”, ministan ya ce, bisa la’akari da bambance-bambancen da Nijeriya take da shi, akwai buƙatar a samar da haɗin kan ƙasa wanda ya zarce ƙabilanci, addini, da siyasa ta hanyar ƙirƙiro da labari mai ban sha’awa na ƙasa, wanda ke ƙarfafa amana da amincewa a tsakanin ‘yan Nijeriya.

Ya ce babban gangamin wayar da kan jama’a na ma’aikatar sa mai taken “Kundin Tsarin Ɗabi’un Nijeriya” wanda nan ba da daɗewa ba Shugaban Ƙasa zai ƙaddamar da shi, ya ƙunshi yarjejeniyar zamantakewa tsakanin ƙasar da ‘yan ƙasar, kuma zai kasance wani shiri na tsarin ɗabi’un ƙasa wanda ke bayyana ‘yan Nijeriya da kuma ƙarfafa halayen su a matsayin su na ’yan ƙasa.

Idris ya ce, “Abu na musamman game da wannan Kundin Ɗabi’un shi ne yarjejeniya ce ta zamantakewa tsakanin gwamnati da ’yan ƙasa kuma tana ɗauke da Manyan Wajibai Bakwai na ƙasar Nijeriya ga ‘yan ƙasa da kuma Alƙawura Bakwai na ‘yan ƙasa ga da ƙasar su. Jigon Kundin Ɗabi’un shi ne dole ne gwamnatin da zaɓaɓɓu da naɗaɗɗun wakilai ke wakilta ta cika wasu muhimman alƙawura don samun muhimman alƙawura daga ‘yan ƙasa.”

Labarai Masu Nasaba

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

Haka kuma ya yi tsokaci kan amana a matsayin ginshiƙin hanyar sadarwa mai inganci kuma mai ɗorewa, yana mai cewa yayin da makomar sadarwa ke nuni ga fasaha, fasahar za ta iya yin tasiri mai ma’ana ne kawai idan aka ɗora ta kan amana.

Ya ce: “Amana ta kasance muhimmin abu wajen gina dangantaka; na kai, na ƙungiya, har ma da na al’umma.

“A matsayin mu na masu magana da yawu, muna buƙatar mu yi ƙoƙari na gaske don gina amana da maido da fata tagari a duk inda muke. Dole ne ginawa da kiyaye amana ya zama wani nauyi da ya rataya a wuyan kowa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan TikTok na KanoMa'aikatar yada labaraiNOA
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Cimma Nasarar Harba Tauraro Na 2 Na Yunhai-3

Next Post

Xi Jinping: Ya Kamata Bangarori Daban Daban Na Sin Da Amurka Su Kara Mu’amala Da Fahimtar Juna

Related

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara
Labarai

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

18 minutes ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

1 hour ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

2 hours ago
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

4 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

6 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

7 hours ago
Next Post
Xi Jinping: Ya Kamata Bangarori Daban Daban Na Sin Da Amurka Su Kara Mu’amala Da Fahimtar Juna

Xi Jinping: Ya Kamata Bangarori Daban Daban Na Sin Da Amurka Su Kara Mu’amala Da Fahimtar Juna

LABARAI MASU NASABA

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

September 14, 2025
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

September 14, 2025
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

September 14, 2025
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

September 14, 2025
Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

September 14, 2025
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

September 14, 2025
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

September 14, 2025
An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.