ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dole Ne Mu Ajiye Bambancin Addini, Ƙabilanci Da Siyasa A Baya – Ministan Yaɗa Labarai

by Sulaiman
2 years ago
Labarai

Wata tabbatacciyar hanya ta samun haɗin kan ‘yan kasa, itace sanya bambancin ƙabilanci, addini, da siyasa a baya, hakan zai samar da ƙarfafa amana da amincewa a tsakanin ‘yan Nijeriya.

Mataimaki na Musamman kan Yaɗa Labarai ga ministan yada labarai, Malam Rabi’u Ibrahim ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai, inda ya ce, Minista Muhammad Idris ya bayyana muhimmancin sanya banbancin dake tsakanin ‘yan kasa a baya domin samun nagartacciyar kasa a yayin da yake jawabi a taron farko na masu magana da yawu wanda Cibiyar Hulɗa Da Jama’a ta Nijeriya (NIPR) ta shirya tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai ta Tarayya a ranar Talata a Abuja.

  • Sojoji Sun Wanke Fursunoni 200 Da Ake Zargin Alaka Da Boko Haram A Borno
  • Masu Satar Mutane Za Mu Dauke Su A Matsayin ‘Yan Ta’adda – Tinubu

Da yake jawabi kan taken taron, wato “Canza Labari, Canza Al’umma”, ministan ya ce, bisa la’akari da bambance-bambancen da Nijeriya take da shi, akwai buƙatar a samar da haɗin kan ƙasa wanda ya zarce ƙabilanci, addini, da siyasa ta hanyar ƙirƙiro da labari mai ban sha’awa na ƙasa, wanda ke ƙarfafa amana da amincewa a tsakanin ‘yan Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Ya ce babban gangamin wayar da kan jama’a na ma’aikatar sa mai taken “Kundin Tsarin Ɗabi’un Nijeriya” wanda nan ba da daɗewa ba Shugaban Ƙasa zai ƙaddamar da shi, ya ƙunshi yarjejeniyar zamantakewa tsakanin ƙasar da ‘yan ƙasar, kuma zai kasance wani shiri na tsarin ɗabi’un ƙasa wanda ke bayyana ‘yan Nijeriya da kuma ƙarfafa halayen su a matsayin su na ’yan ƙasa.

Idris ya ce, “Abu na musamman game da wannan Kundin Ɗabi’un shi ne yarjejeniya ce ta zamantakewa tsakanin gwamnati da ’yan ƙasa kuma tana ɗauke da Manyan Wajibai Bakwai na ƙasar Nijeriya ga ‘yan ƙasa da kuma Alƙawura Bakwai na ‘yan ƙasa ga da ƙasar su. Jigon Kundin Ɗabi’un shi ne dole ne gwamnatin da zaɓaɓɓu da naɗaɗɗun wakilai ke wakilta ta cika wasu muhimman alƙawura don samun muhimman alƙawura daga ‘yan ƙasa.”

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Haka kuma ya yi tsokaci kan amana a matsayin ginshiƙin hanyar sadarwa mai inganci kuma mai ɗorewa, yana mai cewa yayin da makomar sadarwa ke nuni ga fasaha, fasahar za ta iya yin tasiri mai ma’ana ne kawai idan aka ɗora ta kan amana.

Ya ce: “Amana ta kasance muhimmin abu wajen gina dangantaka; na kai, na ƙungiya, har ma da na al’umma.

“A matsayin mu na masu magana da yawu, muna buƙatar mu yi ƙoƙari na gaske don gina amana da maido da fata tagari a duk inda muke. Dole ne ginawa da kiyaye amana ya zama wani nauyi da ya rataya a wuyan kowa.”

Labarai
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Xi Jinping: Ya Kamata Bangarori Daban Daban Na Sin Da Amurka Su Kara Mu’amala Da Fahimtar Juna

Xi Jinping: Ya Kamata Bangarori Daban Daban Na Sin Da Amurka Su Kara Mu’amala Da Fahimtar Juna

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.