• English
  • Business News
Friday, October 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

by Abubakar Sulaiman
4 weeks ago
in Manyan Labarai
0
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar tsaron farin kaya (DSS) ta ba ɗan gwagwarmayar dimokuraɗiyya kuma mawallafin Sahara Reporters, Omoyele Sowore, wa’adin mako guda domin ya janye wani abu da ya wallafa a shafin X (Twitter) kan Shugaba Bola Tinubu, wadda hukumar ta ce “ƙarya ce, ta ɓata suna kuma tana iya tada zaune tsaye.”

A cikin wasiƙar da DSS ta aika masa ranar 7 ga Satumba, 2025, ta zargi Sowore da yin kalaman batanci da cin mutunci ga shugaban ƙasa a wallafar da ya yi ranar 26 ga Agusta, inda ya kira Tinubu “ɓarawo” tare da zargin cewa ya yi wa ’yan Nijeriya ƙarya bayan ya ce cin hanci da rashawa sun daina wanzuwa a gwamnatinsa yayin da yake ziyara a Brazil. Hukumar ta yi gargaɗin cewa rashin bin umarninta zai tilasta mata ɗaukar duk wanivmataki na doka domin kare tsaron ƙasa da zaman lafiya.

  • Kotu Ta Bayar Da Belin Sowore Kan Naira Miliyan 10
  • Buratai Ya Bukaci Kotu Ta Ci Tarar Sowore Naira Biliyan 10 Kan Bata Masa Suna

DSS ta buƙaci Sowore da ya goge rubutun, ya sake wallafa sabuwar sanarwa a shafin X daidai da yadda ya bayyana tun farko, sannan ya buga sanarwar neman afuwa a aƙalla jaridu biyu na ƙasa da tashoshin talabijin biyu masu yaɗa shirye-shirye a faɗin ƙasa. Haka kuma ta umarce shi ya tura rubutaccen bayani zuwa shalƙwatar DSS a Abuja ko ta adireshin imel na hukumar cikin mako guda.

Hukumar ta kuma sanar da cewa ta tura kwafin wasiƙar zuwa ofishin jakadancin Amurka a Abuja, tana nuna cewa lamarin ya ja hankalin diflomasiyyar ƙasashen waje duba da matsayin Sowore na zama a Nijeriya da Amurka. Ta gargaɗe shi da cewa a matsayinsa na wanda ke neman muƙamin siyasa, dole ya nuna ƙwarewa da ladabi a magana da aiki, saboda hakan na da muhimmanci wajen inganta zaman lafiya da tsaro a ƙasar.

DSS ta nanata cewa aikinta na doka shi ne tabbatar da cewa ’yan Nijeriya ba sa samun labaran yaudara ta hanyar yaɗa ƙarya ko farfaganda, tana mai cewa idan Sowore bai janye maganarsa ba cikin wa’adin da aka bayar, to za ta ɗauki matakan da ta dace bisa doka.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

Ina Aka Kwana Batun Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Dazukan Jihar Katsina?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DSSSowore
ShareTweetSendShare
Previous Post

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

Next Post

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

Related

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

5 hours ago
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda
Manyan Labarai

Ina Aka Kwana Batun Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Dazukan Jihar Katsina?

6 hours ago
Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori
Manyan Labarai

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

17 hours ago
Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi
Manyan Labarai

Wata Mata Ta Banka Wa Kanta Wuta Har Lahira A Bauchi

21 hours ago
PENGASSAN Ta Musanta Janyewa Daga Yajin Aiki, Ta Gargaɗi Dangote
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Musanta Janyewa Daga Yajin Aiki, Ta Gargaɗi Dangote

23 hours ago
Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus
Manyan Labarai

Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus

1 day ago
Next Post
Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

‘Yan Nijeriya Na Karbar Sakamakonsu Da Hannun Hagu A Wajen Tinubu – Atiku

October 3, 2025
Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

October 3, 2025
Za mu Inganta Fannin Karatun Alkur’ani – Gwamnan Jigawa

Za mu Inganta Fannin Karatun Alkur’ani – Gwamnan Jigawa

October 3, 2025
Yadda Sanata Barau Ke Samar da Masana Don Ci Gaban Kano

Yadda Sanata Barau Ke Samar da Masana Don Ci Gaban Kano

October 3, 2025
Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

October 3, 2025
Ƴansanda Sun Fara Aiwatar Da Dokar Sanya Baƙin Gilashi Mota A Legas

Ƴansanda Sun Fara Aiwatar Da Dokar Sanya Baƙin Gilashi Mota A Legas

October 3, 2025
Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

October 3, 2025
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

October 3, 2025
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Ina Aka Kwana Batun Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Dazukan Jihar Katsina?

October 3, 2025
Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin

Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin

October 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.