• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

by Abubakar Sulaiman
2 months ago
Sowore

Hukumar tsaron farin kaya (DSS) ta ba ɗan gwagwarmayar dimokuraɗiyya kuma mawallafin Sahara Reporters, Omoyele Sowore, wa’adin mako guda domin ya janye wani abu da ya wallafa a shafin X (Twitter) kan Shugaba Bola Tinubu, wadda hukumar ta ce “ƙarya ce, ta ɓata suna kuma tana iya tada zaune tsaye.”

A cikin wasiƙar da DSS ta aika masa ranar 7 ga Satumba, 2025, ta zargi Sowore da yin kalaman batanci da cin mutunci ga shugaban ƙasa a wallafar da ya yi ranar 26 ga Agusta, inda ya kira Tinubu “ɓarawo” tare da zargin cewa ya yi wa ’yan Nijeriya ƙarya bayan ya ce cin hanci da rashawa sun daina wanzuwa a gwamnatinsa yayin da yake ziyara a Brazil. Hukumar ta yi gargaɗin cewa rashin bin umarninta zai tilasta mata ɗaukar duk wanivmataki na doka domin kare tsaron ƙasa da zaman lafiya.

  • Kotu Ta Bayar Da Belin Sowore Kan Naira Miliyan 10
  • Buratai Ya Bukaci Kotu Ta Ci Tarar Sowore Naira Biliyan 10 Kan Bata Masa Suna

DSS ta buƙaci Sowore da ya goge rubutun, ya sake wallafa sabuwar sanarwa a shafin X daidai da yadda ya bayyana tun farko, sannan ya buga sanarwar neman afuwa a aƙalla jaridu biyu na ƙasa da tashoshin talabijin biyu masu yaɗa shirye-shirye a faɗin ƙasa. Haka kuma ta umarce shi ya tura rubutaccen bayani zuwa shalƙwatar DSS a Abuja ko ta adireshin imel na hukumar cikin mako guda.

Hukumar ta kuma sanar da cewa ta tura kwafin wasiƙar zuwa ofishin jakadancin Amurka a Abuja, tana nuna cewa lamarin ya ja hankalin diflomasiyyar ƙasashen waje duba da matsayin Sowore na zama a Nijeriya da Amurka. Ta gargaɗe shi da cewa a matsayinsa na wanda ke neman muƙamin siyasa, dole ya nuna ƙwarewa da ladabi a magana da aiki, saboda hakan na da muhimmanci wajen inganta zaman lafiya da tsaro a ƙasar.

DSS ta nanata cewa aikinta na doka shi ne tabbatar da cewa ’yan Nijeriya ba sa samun labaran yaudara ta hanyar yaɗa ƙarya ko farfaganda, tana mai cewa idan Sowore bai janye maganarsa ba cikin wa’adin da aka bayar, to za ta ɗauki matakan da ta dace bisa doka.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar
Manyan Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

October 24, 2025
Next Post
Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.