• English
  • Business News
Sunday, October 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

by Sulaiman
3 years ago
DSS

Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta ce ta gudanar da wani samame tare da hadin guiwar sauran jami’an tsaro a jihar Kogi a ranar Lahadi, 26 ga Maris, 2023, inda rundunar ta kama wasu gungun masu aikata laifuka su shida a Gegu Beki, a Lokoja kan hanyar Abuja.

Mai magana da yawun hukumar DSS, Dakta Peter Afunanya, a wata sanarwa da ya fitar a daren Lahadi ya ce, mutane shidan sun hada da kanal AU Suleiman (mai ritaya), Barista MK Aminu, Kabir Abdullahi, Isah Umar, Kadir Echi da Adama Abdulkarim.

  • NDLEA Ta Cafke Wani Fitaccen Dan Kasuwa Da Hodar Iblis Zuwa Kasar Waje

Makaman da aka kwato daga hannunsu sun hada da bindiga kirar famfo daya, kwalbasar alburusai 4, kwalbasar alburusai ta AK47 guda daya da jimillar kudi Naira N11,030.

Har ila yau, a ranar 25 ga Maris, 2023, jami’an sun kama wani matashi mai shekaru 20 da ake zargi da yin garkuwa da mutane, Haruna Adamu, a kauyen Fotta da ke karamar hukumar Gombi ta jihar Adamawa.

Hukumar ta DSS ta ce, ta kwato bindiga kirar AK-47 guda daya, kwalbasar alburusai daya da harsashi mai tsawon 7.62mm guda hudu daga hannun wanda ake zargin.

LABARAI MASU NASABA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

Haka kuma a ranar 23 ga Maris, 2023, an kama wani mai suna Aminu Ibrahim, wanda ake zargin dan bindiga ne a hanyar Kubwa Expressway, Abuja a lokacin da yake kan hanyarsa daga jihar Nasarawa don kai alburusai 432 mai girman 7.62 x39mm da aka boye a cikin galan din manja mai fadin lita hudu zai kai wa ‘yan bindiga da ke jihar Neja. An kuma karbo kudi Naira N21,400 daga hannun wanda ake zargin.

Hakazalika, a ranar 22 ga Maris, 2023, an kama Babangida Ibrahim, mai jigilar makamai zuwa ga ‘yan bindiga a jihar Zamfara a Bukuru a karamar hukumar Jos ta Kudu, jihar Filato.

Kayayyakin da aka kwato daga hannunsa sun hada da harsashi 468 mai girman harsashi 7.62 x 39mm da kudi naira N21,090.

Dukkan wadanda ake zargin za a gurfanar da su a gaban kotu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza

Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza

October 11, 2025
Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal

Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal

October 11, 2025
Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata

Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata

October 11, 2025
Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Takunkumin Da Amurka Ta Sanyawa Masana’antunta 

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Takunkumin Da Amurka Ta Sanyawa Masana’antunta 

October 11, 2025
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025

October 11, 2025
Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

October 11, 2025
An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

October 11, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.