• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

by Sulaiman
3 years ago
DSS

Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta ce ta gudanar da wani samame tare da hadin guiwar sauran jami’an tsaro a jihar Kogi a ranar Lahadi, 26 ga Maris, 2023, inda rundunar ta kama wasu gungun masu aikata laifuka su shida a Gegu Beki, a Lokoja kan hanyar Abuja.

Mai magana da yawun hukumar DSS, Dakta Peter Afunanya, a wata sanarwa da ya fitar a daren Lahadi ya ce, mutane shidan sun hada da kanal AU Suleiman (mai ritaya), Barista MK Aminu, Kabir Abdullahi, Isah Umar, Kadir Echi da Adama Abdulkarim.

  • NDLEA Ta Cafke Wani Fitaccen Dan Kasuwa Da Hodar Iblis Zuwa Kasar Waje

Makaman da aka kwato daga hannunsu sun hada da bindiga kirar famfo daya, kwalbasar alburusai 4, kwalbasar alburusai ta AK47 guda daya da jimillar kudi Naira N11,030.

Har ila yau, a ranar 25 ga Maris, 2023, jami’an sun kama wani matashi mai shekaru 20 da ake zargi da yin garkuwa da mutane, Haruna Adamu, a kauyen Fotta da ke karamar hukumar Gombi ta jihar Adamawa.

Hukumar ta DSS ta ce, ta kwato bindiga kirar AK-47 guda daya, kwalbasar alburusai daya da harsashi mai tsawon 7.62mm guda hudu daga hannun wanda ake zargin.

LABARAI MASU NASABA

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Haka kuma a ranar 23 ga Maris, 2023, an kama wani mai suna Aminu Ibrahim, wanda ake zargin dan bindiga ne a hanyar Kubwa Expressway, Abuja a lokacin da yake kan hanyarsa daga jihar Nasarawa don kai alburusai 432 mai girman 7.62 x39mm da aka boye a cikin galan din manja mai fadin lita hudu zai kai wa ‘yan bindiga da ke jihar Neja. An kuma karbo kudi Naira N21,400 daga hannun wanda ake zargin.

Hakazalika, a ranar 22 ga Maris, 2023, an kama Babangida Ibrahim, mai jigilar makamai zuwa ga ‘yan bindiga a jihar Zamfara a Bukuru a karamar hukumar Jos ta Kudu, jihar Filato.

Kayayyakin da aka kwato daga hannunsa sun hada da harsashi 468 mai girman harsashi 7.62 x 39mm da kudi naira N21,090.

Dukkan wadanda ake zargin za a gurfanar da su a gaban kotu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
Manyan Labarai

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
Manyan Labarai

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit
Labarai

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Next Post
SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

LABARAI MASU NASABA

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025
Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.