• Leadership Hausa
Monday, May 29, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

by Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta ce ta gudanar da wani samame tare da hadin guiwar sauran jami’an tsaro a jihar Kogi a ranar Lahadi, 26 ga Maris, 2023, inda rundunar ta kama wasu gungun masu aikata laifuka su shida a Gegu Beki, a Lokoja kan hanyar Abuja.

Mai magana da yawun hukumar DSS, Dakta Peter Afunanya, a wata sanarwa da ya fitar a daren Lahadi ya ce, mutane shidan sun hada da kanal AU Suleiman (mai ritaya), Barista MK Aminu, Kabir Abdullahi, Isah Umar, Kadir Echi da Adama Abdulkarim.

  • NDLEA Ta Cafke Wani Fitaccen Dan Kasuwa Da Hodar Iblis Zuwa Kasar Waje

Makaman da aka kwato daga hannunsu sun hada da bindiga kirar famfo daya, kwalbasar alburusai 4, kwalbasar alburusai ta AK47 guda daya da jimillar kudi Naira N11,030.

Har ila yau, a ranar 25 ga Maris, 2023, jami’an sun kama wani matashi mai shekaru 20 da ake zargi da yin garkuwa da mutane, Haruna Adamu, a kauyen Fotta da ke karamar hukumar Gombi ta jihar Adamawa.

Hukumar ta DSS ta ce, ta kwato bindiga kirar AK-47 guda daya, kwalbasar alburusai daya da harsashi mai tsawon 7.62mm guda hudu daga hannun wanda ake zargin.

Labarai Masu Nasaba

Da Dumi-dumi: Justis Hafsat Ta Rantsar Da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri

Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

Haka kuma a ranar 23 ga Maris, 2023, an kama wani mai suna Aminu Ibrahim, wanda ake zargin dan bindiga ne a hanyar Kubwa Expressway, Abuja a lokacin da yake kan hanyarsa daga jihar Nasarawa don kai alburusai 432 mai girman 7.62 x39mm da aka boye a cikin galan din manja mai fadin lita hudu zai kai wa ‘yan bindiga da ke jihar Neja. An kuma karbo kudi Naira N21,400 daga hannun wanda ake zargin.

Hakazalika, a ranar 22 ga Maris, 2023, an kama Babangida Ibrahim, mai jigilar makamai zuwa ga ‘yan bindiga a jihar Zamfara a Bukuru a karamar hukumar Jos ta Kudu, jihar Filato.

Kayayyakin da aka kwato daga hannunsa sun hada da harsashi 468 mai girman harsashi 7.62 x 39mm da kudi naira N21,090.

Dukkan wadanda ake zargin za a gurfanar da su a gaban kotu.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 5

Next Post

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

Related

Da Dumi-dumi: Justis Hafsat Ta Rantsar Da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri
Labarai

Da Dumi-dumi: Justis Hafsat Ta Rantsar Da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri

12 mins ago
Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16
Labarai

Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

2 hours ago
A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15
Labarai

A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15

2 hours ago
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 
Labarai

Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

3 hours ago
Bankwana Da Gwamnatin Buhari: Hukumar Tsaron Cikin Gida Ta Kara Wa Jami’ai 17,331 Matsayi
Labarai

Bankwana Da Gwamnatin Buhari: Hukumar Tsaron Cikin Gida Ta Kara Wa Jami’ai 17,331 Matsayi

3 hours ago
Kwana Guda Ya Sauka, El-Rufai Ya Haramta Kungiyar Kudancin Kaduna
Labarai

Kwana Guda Ya Sauka, El-Rufai Ya Haramta Kungiyar Kudancin Kaduna

5 hours ago
Next Post
SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

LABARAI MASU NASABA

Da Dumi-dumi: Justis Hafsat Ta Rantsar Da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri

Da Dumi-dumi: Justis Hafsat Ta Rantsar Da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri

May 29, 2023
Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

May 29, 2023
A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15

A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15

May 29, 2023
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

May 29, 2023
Bankwana Da Gwamnatin Buhari: Hukumar Tsaron Cikin Gida Ta Kara Wa Jami’ai 17,331 Matsayi

Bankwana Da Gwamnatin Buhari: Hukumar Tsaron Cikin Gida Ta Kara Wa Jami’ai 17,331 Matsayi

May 29, 2023
Gwamnati Ta Samar Da Tan 89,512 Na Irin Noma A Bana – Minista

Gwamnati Ta Samar Da Tan 89,512 Na Irin Noma A Bana – Minista

May 29, 2023
Kwana Guda Ya Sauka, El-Rufai Ya Haramta Kungiyar Kudancin Kaduna

Kwana Guda Ya Sauka, El-Rufai Ya Haramta Kungiyar Kudancin Kaduna

May 29, 2023
Buhari Ya Nada Sha’aban Mukamin Babban Sakataren Hukumar Kula Da Almajirai Ta Nijeriya

Buhari Ya Nada Sha’aban Mukamin Babban Sakataren Hukumar Kula Da Almajirai Ta Nijeriya

May 28, 2023
An Wallafa Littafin Dake Kunshe Da Mukalolin Shugaba Xi Kan Dogaro Da Kai A Fannin Kimiyya Da Fasaha

An Wallafa Littafin Dake Kunshe Da Mukalolin Shugaba Xi Kan Dogaro Da Kai A Fannin Kimiyya Da Fasaha

May 28, 2023
Ganduje Yayi Jawabin Bankwana Tare Da Shirin Mika Mulki A Yau Lahadi

Ganduje Yayi Jawabin Bankwana Tare Da Shirin Mika Mulki A Yau Lahadi

May 28, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.