• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dubban Mambobin Jam’iyyar APC Sun Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar PDP A Bauchi

A Bayyana Sunayen Wadanda Suka Fice Din - APC

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Siyasa
0
Dubban Mambobin Jam’iyyar APC Sun Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar PDP A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban matasa na jam’iyyar APC a Jihar Bauchi, Alhaji Adamu Dako tare da magoya bayansa sun ayyana ficewa daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar PDP.

Da ya ke jawabi a lokacin yankan katin shiga PDP a ofishin jam’iyyar da ke karamar hukumar Bauchi a ranar Litinin, Dako ya bayyana cewar abubuwa ba su tafiya daidai a cikin APC don haka ne ya yanke shawarar ficewa.

  • Gwamnatin Legas Ta Rufe Wata Makaranta Saboda Mutuwar Dalibi
  • An Fitar Da Rahoton Nazari Game Da Yanayin Aiki Na Alummun Yankin Xinjiang

“Yau ni da magoya bayana sama da dubu bakwai (7,000) mun ayyana ficewa daga jam’iyyar APC zuwa PDP.

“Na kasance a da baya jagora a cikin jam’iyyar APC, amma cikin ikon Allah na fice daga jam’iyyar sakamakon matsaloli da suke jibge a cikinta. Na yi nadamar bata shekara da shekaru a cikin jam’iyyar APC.”

Alhaji Dako ya ce, dukkanin alamun fadin jam’iyyar APC a jihar Bauchi ya tabbata, yana mai cewa, hatta zabin da jam’iyyar ta yi wa dan takarar gwamnan Sadik Baba Abubakar alamu ne da ke nuna ba za ta iya samun nasara a zaben gwamnan jihar ba.

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

“Wannan dan takara da jam’iyyar APC ta ayyana kalubale ne a gabanta a zaben 2023.”

“Duk wanda ya san yadda aka yi hadaka aka kafa APC, yanzu kowa ya san ba jam’iyya ake yi ba son zuciya kawai ake bi. APC ta mutu murus a jihar Bauchi. Na shigo jam’iyyar PDP da kyakkyawar manufa.”

Ya ce, sun shiga PDP ne lura da irin nasarorin da gwamnan jihar Bala Muhammad ya cimma na kyautata jihar.

Don haka ne ya nuna kwarin guiwarsa na cewa gwamna Bala zai sake samun nasara a karo na biyu tare da kiran al’umma da su mara wa gwamnan ba.

Da yake amsar wadanda suka sauya shekar, shugaban jam’iyyar PDP a karamar hukumar Bauchi, Alhaji Abdulkadir Alin Bababa, ya sanar da cewa, jam’iyyar ta karbi sabbin mambobin jam’iyyar APC da suka sauya sheka zuwa PDP su dubu bakwai.

Shugaban wanda ya samu wakilcin, mataimakinsa Sani Ahmad, tare da sauran shugabanin jam’iyyar a karamar hukumar, ya bai wa wanda suka dawo jam’iyyar tabbacin samun adalci daga wajensu tare da share musu hawayen matsalolin da suka zo da su, ya rokesu da su taimaka domin samun nasarar PDP a 2023.

Shi ma a jawabinsa na lale ga sabbin mambobin, babban mai bai wa gwamnan jihar Bauchi shawara kan harkokin siyasa, Hon. Abubakar Faggo, ya bayyana cewar yadda ake shigowa cikin jam’iyyar PDP alamu ne da ke nuna irin gamsuwa da salon mulkin gwamna Bala.

Ya ce, tabbas gwamna Bala Muhammad na gudanar da kyawawan ayyukan bunkasa jihar Bauchi, don haka ne ya nemi jama’ar jihar da su kara ba shi dama domin kyautata jihar, ya kuma nuna cewa tabbas wadanda suka dawo jam’iyyar za su samu goyon baya daga PDP.

Faggo, ya nuna cewa jam’iyyar APC bata kyauta wa mambobinta, don haka ne ma suke ta komawa cikin PDP.

“Mu a PDP akwai adalci, don haka kun zo lallai kuma za a muku adalci.”

Da ya ke maida martani kan wannan matakin, jami’in watsa labarai na jam’iyyar APC a jihar Bauchi, Alhaji Adamu Aliyu Jalla, ya ce suna da ja man cewa mutum 7,000 sun fice daga jam’iyyarsu.

Ya ce, kowa na da ‘yancin sauya sheka, amma ya ce da dandazon mutum kaza fita wannan kuma akwai bukatar tabbatarwar kafin amincewa.

“Farfagandar siyasa ce kawai. Mutum 7000 wasa ne. Mu ba mu da bayanin cewa wannan adadin sun fita a jam’iyyunmu. Don haka muna kalubala tarsa da ya bayyana sunayen mutum 7000 din.”

Ya ce babu gaskiya na cewa ana gudanar da mulki cikin jam’iyyar APC bisa rashin adalci, ya nuna cewa suna da karfin da za su iya cin zaben 2023 tare da goyon bayan al’ummar jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdalciAPCBala MohammedBauchiCi GabaPDPSauya Sheka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Legas Ta Rufe Wata Makaranta Saboda Mutuwar Dalibi

Next Post

NCC Ta Bai Wa Kamfanonin Sadarwa Kwana 30 Don Warware Matsalolin Masu Amfani Da Layukansu

Related

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

2 days ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

3 days ago
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

6 days ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

7 days ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

1 week ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

1 week ago
Next Post
NCC Ta Bai Wa Kamfanonin Sadarwa Kwana 30 Don Warware Matsalolin Masu Amfani Da Layukansu

NCC Ta Bai Wa Kamfanonin Sadarwa Kwana 30 Don Warware Matsalolin Masu Amfani Da Layukansu

LABARAI MASU NASABA

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.