• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dubban Mambobin Jam’iyyar APC Sun Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar PDP A Bauchi

A Bayyana Sunayen Wadanda Suka Fice Din - APC

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Siyasa
0
Dubban Mambobin Jam’iyyar APC Sun Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar PDP A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban matasa na jam’iyyar APC a Jihar Bauchi, Alhaji Adamu Dako tare da magoya bayansa sun ayyana ficewa daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar PDP.

Da ya ke jawabi a lokacin yankan katin shiga PDP a ofishin jam’iyyar da ke karamar hukumar Bauchi a ranar Litinin, Dako ya bayyana cewar abubuwa ba su tafiya daidai a cikin APC don haka ne ya yanke shawarar ficewa.

  • Gwamnatin Legas Ta Rufe Wata Makaranta Saboda Mutuwar Dalibi
  • An Fitar Da Rahoton Nazari Game Da Yanayin Aiki Na Alummun Yankin Xinjiang

“Yau ni da magoya bayana sama da dubu bakwai (7,000) mun ayyana ficewa daga jam’iyyar APC zuwa PDP.

“Na kasance a da baya jagora a cikin jam’iyyar APC, amma cikin ikon Allah na fice daga jam’iyyar sakamakon matsaloli da suke jibge a cikinta. Na yi nadamar bata shekara da shekaru a cikin jam’iyyar APC.”

Alhaji Dako ya ce, dukkanin alamun fadin jam’iyyar APC a jihar Bauchi ya tabbata, yana mai cewa, hatta zabin da jam’iyyar ta yi wa dan takarar gwamnan Sadik Baba Abubakar alamu ne da ke nuna ba za ta iya samun nasara a zaben gwamnan jihar ba.

Labarai Masu Nasaba

Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

“Wannan dan takara da jam’iyyar APC ta ayyana kalubale ne a gabanta a zaben 2023.”

“Duk wanda ya san yadda aka yi hadaka aka kafa APC, yanzu kowa ya san ba jam’iyya ake yi ba son zuciya kawai ake bi. APC ta mutu murus a jihar Bauchi. Na shigo jam’iyyar PDP da kyakkyawar manufa.”

Ya ce, sun shiga PDP ne lura da irin nasarorin da gwamnan jihar Bala Muhammad ya cimma na kyautata jihar.

Don haka ne ya nuna kwarin guiwarsa na cewa gwamna Bala zai sake samun nasara a karo na biyu tare da kiran al’umma da su mara wa gwamnan ba.

Da yake amsar wadanda suka sauya shekar, shugaban jam’iyyar PDP a karamar hukumar Bauchi, Alhaji Abdulkadir Alin Bababa, ya sanar da cewa, jam’iyyar ta karbi sabbin mambobin jam’iyyar APC da suka sauya sheka zuwa PDP su dubu bakwai.

Shugaban wanda ya samu wakilcin, mataimakinsa Sani Ahmad, tare da sauran shugabanin jam’iyyar a karamar hukumar, ya bai wa wanda suka dawo jam’iyyar tabbacin samun adalci daga wajensu tare da share musu hawayen matsalolin da suka zo da su, ya rokesu da su taimaka domin samun nasarar PDP a 2023.

Shi ma a jawabinsa na lale ga sabbin mambobin, babban mai bai wa gwamnan jihar Bauchi shawara kan harkokin siyasa, Hon. Abubakar Faggo, ya bayyana cewar yadda ake shigowa cikin jam’iyyar PDP alamu ne da ke nuna irin gamsuwa da salon mulkin gwamna Bala.

Ya ce, tabbas gwamna Bala Muhammad na gudanar da kyawawan ayyukan bunkasa jihar Bauchi, don haka ne ya nemi jama’ar jihar da su kara ba shi dama domin kyautata jihar, ya kuma nuna cewa tabbas wadanda suka dawo jam’iyyar za su samu goyon baya daga PDP.

Faggo, ya nuna cewa jam’iyyar APC bata kyauta wa mambobinta, don haka ne ma suke ta komawa cikin PDP.

“Mu a PDP akwai adalci, don haka kun zo lallai kuma za a muku adalci.”

Da ya ke maida martani kan wannan matakin, jami’in watsa labarai na jam’iyyar APC a jihar Bauchi, Alhaji Adamu Aliyu Jalla, ya ce suna da ja man cewa mutum 7,000 sun fice daga jam’iyyarsu.

Ya ce, kowa na da ‘yancin sauya sheka, amma ya ce da dandazon mutum kaza fita wannan kuma akwai bukatar tabbatarwar kafin amincewa.

“Farfagandar siyasa ce kawai. Mutum 7000 wasa ne. Mu ba mu da bayanin cewa wannan adadin sun fita a jam’iyyunmu. Don haka muna kalubala tarsa da ya bayyana sunayen mutum 7000 din.”

Ya ce babu gaskiya na cewa ana gudanar da mulki cikin jam’iyyar APC bisa rashin adalci, ya nuna cewa suna da karfin da za su iya cin zaben 2023 tare da goyon bayan al’ummar jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdalciAPCBala MohammedBauchiCi GabaPDPSauya Sheka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Legas Ta Rufe Wata Makaranta Saboda Mutuwar Dalibi

Next Post

NCC Ta Bai Wa Kamfanonin Sadarwa Kwana 30 Don Warware Matsalolin Masu Amfani Da Layukansu

Related

Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa
Siyasa

Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

5 hours ago
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa
Siyasa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

21 hours ago
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili
Siyasa

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

23 hours ago
Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa
Siyasa

Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa

1 day ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Labarai

2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC

2 days ago
Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
Siyasa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

3 days ago
Next Post
NCC Ta Bai Wa Kamfanonin Sadarwa Kwana 30 Don Warware Matsalolin Masu Amfani Da Layukansu

NCC Ta Bai Wa Kamfanonin Sadarwa Kwana 30 Don Warware Matsalolin Masu Amfani Da Layukansu

LABARAI MASU NASABA

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

August 2, 2025
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

August 2, 2025
Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

August 2, 2025
An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo

An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.