• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dubban Manoma Za Su Amfana Da Fasahar Adana Tumatir A Kano

byAbubakar Abba
3 years ago
Manoma

Kimanin manonan tumatir dubu uku da ke Jihar Kano, za su amfana da fasahar adana tumatir a karkashin shirin da wata kungiya mai zaman kanta, mai suna ‘Pydera Global YieldWise Nigeria’ ta kirkiro da shi.

Kungiyar ta fito da shirin ne don rage wa manoman na tumatir da ke jihar yawan asarar da suke yi, a kasuwar tumatirin din.

  • Dimbin Ribar Noman Inabi A Nijeriya

Aikin, wanda kuma gidauniyar Rockefeller ce ta samar da kudi don yinsa, an kirkiro da shi ne don magance asarar da manoman na tumatir suke yi a lokacin da suka dasa shi da kuma kan sauran amfanin gona da ake shuka wa a kasar nan.

Daraktan shirin Lekan Tobi ne ya sanar da hakan a lokacin kaddamar da shirin a kauyen Kwanar Agalawa da ke cikin karamar hukumar Garunmalam da ke jihar ta Kano a ranar Talatar da ta wuce.

Kamfanin dillancin labarai na kasa, ya ruwaito cewar, kauyen na Kwanar Agalawa, yana daya daga cikin yankunan da ake noma tumatir mai yawa a jihar.
A cewar Mista Tobi, kungiyar ta yanke shawarar kirkiro da aikin ne don shawo kan kalubalen da manoman suke fuskan ta ne a yankin.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Ya ci gaba da cewa, manoman tumatir su dubu uku da aka zabo daga cikin kungiyoyin manoma arba’in da hudu ne za su amfana da shirin, inda za a samar musu da wajen adana tumatir da kuma sarrafa shi.

Ya bayyana cewar, manoman suna da zabin samo musu sayen tumatir din su da kuma samun ingantaccen irin tumatir don samun yin noma mai riba.
Ya yi nuni da cewa, a bisa fasahar, za kuma a koyawa manoman yadda za su adana Kokumba da Albasa da Shinkafa da masara da sauransu.

Shi kuwa a nasa jawabain a wurin taron, Mataimakin gwamnan jihar Kano Alhaji Nasiru Gawuna, ya ce gwamnatin jihar zata ci gaba da baiwa fannin aikin gona fifiko, musamman don samar da wadataccen abinci a jihar.

Mataimakin gwamnan wanda babban sakatatare a ma’aikatar aikin gona da albarkantu na jihar Aminu Garba ya wakilce shi a wurin taron mataimakin gwamnan ya kuma ya ba a kan kirkiro da shirin na YieldWise Nijeriya.

Taron ya kuma samu halartar masu noma tumatir da sauran masu ruwa da tsaki a fannin, harda wakilan da suka fito daga jihar Jigawa da Katsina da Kaduna da kuma Folato.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Yadda Ridi Da Kwai Ke Gyara Jikin Mace (2)

Yadda Ridi Da Kwai Ke Gyara Jikin Mace (2)

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version