• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Ɗan Siyasar Da Ya Shiga Rigar Kwankwaso Ya Kauce Hanya Zai Gani A 2027 – Alhaji Ibrahim

‘Yan Arewa Mu Yi Wa Kanmu Karatun Ta-natsu, In Ji Shi

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Siyasa
0
Duk Ɗan Siyasar Da Ya Shiga Rigar Kwankwaso Ya Kauce Hanya Zai Gani A 2027 – Alhaji Ibrahim
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar Matasan Arewa da ke Kudancin Nijeriya ta yi gargaɗin cewa duk wani ɗan siyasa da ya shiga rigar Jagoran Jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya lashe zaɓe kuma daga bisani ya kauce wa hanyar da Kwankwason ke bi, zai gani a ƙwaryar cin tuwonsa idan Allah ya kai mu zaɓen 2027.

Ƙungiyar ta yi gargaɗin ne a wani taron manema labarai na musamman da ta kira a Kano domin faɗakar da ‘yan siyasa da kuma ‘yan arewa game da muhimmancin nuna kishin yankin musamman a yanzu da aka rantsar da sabuwar gwamnati a ƙasa baki ɗaya.
Da yake ƙarin haske ga wakilinmu bayan kammala taron, shugaban ƙungiyar, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci ya yi nuni da cewa, akwai ‘yan siyasa da dama da suka ci alfarmar jagoran na NNPP, Sanata Kwankwaso suka samu kujerun majalisa, “amma mun san ‘yan siyasar Nijeriya suna da wata ɗabi’a, za su shiga rigar mutum su samu abin da suke so, da zarar sun samu sai su kauce. To muna kira ga waɗanda suka shiga rigar ɗan kishin mutanen arewa da babu kamarsa wajen nuna wa al’ummarmu kishi, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, suka lashe zaɓe musamman a majalisun dokoki na ƙasa da na jihohi cewa kar su ci amana su kauce wa hanyarsa. Idan suka ƙi ji, to kowa ya sani, mu talakawa da muke da ƙuri’u a hannunmu za mu yi tsayin daka wajen ganin ba su koma ba, kowa zai gani a ƙwaryar cin tuwonsa.

  • Shugaban Nijeriya Na 16: Jan Aikin Da Ke Gaban Jagaban

“Abin da ya sa muke wannan kiran a kan Kwankwaso shi ne, duk cikin ‘yan siyasar da muke da su a arewa babu wanda yake nuna kishin al’umma a fili irin Kwankwaso. Mu da muke kudu, mun shaida irin yadda yake kai-komo a duk lokacin da aka ce ga wani abu ya samu wani ɗan arewa a can. Idan ba a manta ba, a zamanin da ɗan takarar shugaban ƙasa na LP, Peter Obi yake Gwamnan Anambara, ya bayar da umarni ga kowane ɗan arewa ya yi wata shaida da za a riƙa gane shi da ita. Ba tare da wani ɓata lokaci ba, shi ma Kwankwaso ya ce kowane Ibo da ke Kano ya yi uniform da za a riƙa gane su da shi.

“Haka nan lokacin da aka tsare mutanenmu a can. ƙungiyarmu musamman a Legas ita take ruwa da tsaki wurin fitar da mutanenmu da aka tsare daga gidan yari. Kuɗin da ake cin tarar mutanenmu daga kan dubu ɗaya har zuwa dubu ɗari (100,000) duk nakan yi ƙoƙarin biya ba tare da na saurari wani mai muƙami ko wata gwamnati ba. Aƙalla yanzu tsakanin kudu da arewa muna da mambobi sama da dubu takwas. Muna iya bakin ƙoƙari wajen ganin mun kare haƙƙin arewa, shi ya sa muke ƙara jaddada kira ga duk waɗanda suka kamata cewa mu yi wa kanmu karatun ta-natsu, idan Allah ya kai mu 2027 mu haɗa kai mu tabbatar da nasarar Sanata Kwankwaso a matsayinsa na ɗan kishin al’umma da ƙasa baki ɗaya.” In ji shi.

Wakazalika, Alhaji Ya’u Ibrahim Galadanci, ya buƙaci ‘yan siyasar da ke mayar da ‘ya`yan talakawa ‘yan shaye-shaye su sani Allah yana kallonsu kuma al’umma ba za ta ƙyale ba. “Sai dai su tura ‘ya’yansu zuwa ƙasashen Turai su yi karatu a can, amma sai su haɗa `ya’yan talakawa da kayan shaye-shaye don su riƙa amfani da su ana cin mutuncin masu mutunci. To, duk wannan ya kamata al’umma ta fito ta yi maganinsu ta hanyar ƙin zaɓarsu, idan aka yi haka za a samu sauƙi sosai ko kuma a magance lamarin.” Kamar yadda ya bayyana.

Labarai Masu Nasaba

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaKwankwasoSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

Next Post

Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

Related

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

20 hours ago
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

2 days ago
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

5 days ago
Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 
Siyasa

Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 

5 days ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

5 days ago
Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

5 days ago
Next Post
Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.