ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Ɗan Siyasar Da Ya Shiga Rigar Kwankwaso Ya Kauce Hanya Zai Gani A 2027 – Alhaji Ibrahim

‘Yan Arewa Mu Yi Wa Kanmu Karatun Ta-natsu, In Ji Shi

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Siyasa

Ƙungiyar Matasan Arewa da ke Kudancin Nijeriya ta yi gargaɗin cewa duk wani ɗan siyasa da ya shiga rigar Jagoran Jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya lashe zaɓe kuma daga bisani ya kauce wa hanyar da Kwankwason ke bi, zai gani a ƙwaryar cin tuwonsa idan Allah ya kai mu zaɓen 2027.

Ƙungiyar ta yi gargaɗin ne a wani taron manema labarai na musamman da ta kira a Kano domin faɗakar da ‘yan siyasa da kuma ‘yan arewa game da muhimmancin nuna kishin yankin musamman a yanzu da aka rantsar da sabuwar gwamnati a ƙasa baki ɗaya.
Da yake ƙarin haske ga wakilinmu bayan kammala taron, shugaban ƙungiyar, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci ya yi nuni da cewa, akwai ‘yan siyasa da dama da suka ci alfarmar jagoran na NNPP, Sanata Kwankwaso suka samu kujerun majalisa, “amma mun san ‘yan siyasar Nijeriya suna da wata ɗabi’a, za su shiga rigar mutum su samu abin da suke so, da zarar sun samu sai su kauce. To muna kira ga waɗanda suka shiga rigar ɗan kishin mutanen arewa da babu kamarsa wajen nuna wa al’ummarmu kishi, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, suka lashe zaɓe musamman a majalisun dokoki na ƙasa da na jihohi cewa kar su ci amana su kauce wa hanyarsa. Idan suka ƙi ji, to kowa ya sani, mu talakawa da muke da ƙuri’u a hannunmu za mu yi tsayin daka wajen ganin ba su koma ba, kowa zai gani a ƙwaryar cin tuwonsa.

  • Shugaban Nijeriya Na 16: Jan Aikin Da Ke Gaban Jagaban

“Abin da ya sa muke wannan kiran a kan Kwankwaso shi ne, duk cikin ‘yan siyasar da muke da su a arewa babu wanda yake nuna kishin al’umma a fili irin Kwankwaso. Mu da muke kudu, mun shaida irin yadda yake kai-komo a duk lokacin da aka ce ga wani abu ya samu wani ɗan arewa a can. Idan ba a manta ba, a zamanin da ɗan takarar shugaban ƙasa na LP, Peter Obi yake Gwamnan Anambara, ya bayar da umarni ga kowane ɗan arewa ya yi wata shaida da za a riƙa gane shi da ita. Ba tare da wani ɓata lokaci ba, shi ma Kwankwaso ya ce kowane Ibo da ke Kano ya yi uniform da za a riƙa gane su da shi.

ADVERTISEMENT

“Haka nan lokacin da aka tsare mutanenmu a can. ƙungiyarmu musamman a Legas ita take ruwa da tsaki wurin fitar da mutanenmu da aka tsare daga gidan yari. Kuɗin da ake cin tarar mutanenmu daga kan dubu ɗaya har zuwa dubu ɗari (100,000) duk nakan yi ƙoƙarin biya ba tare da na saurari wani mai muƙami ko wata gwamnati ba. Aƙalla yanzu tsakanin kudu da arewa muna da mambobi sama da dubu takwas. Muna iya bakin ƙoƙari wajen ganin mun kare haƙƙin arewa, shi ya sa muke ƙara jaddada kira ga duk waɗanda suka kamata cewa mu yi wa kanmu karatun ta-natsu, idan Allah ya kai mu 2027 mu haɗa kai mu tabbatar da nasarar Sanata Kwankwaso a matsayinsa na ɗan kishin al’umma da ƙasa baki ɗaya.” In ji shi.

Wakazalika, Alhaji Ya’u Ibrahim Galadanci, ya buƙaci ‘yan siyasar da ke mayar da ‘ya`yan talakawa ‘yan shaye-shaye su sani Allah yana kallonsu kuma al’umma ba za ta ƙyale ba. “Sai dai su tura ‘ya’yansu zuwa ƙasashen Turai su yi karatu a can, amma sai su haɗa `ya’yan talakawa da kayan shaye-shaye don su riƙa amfani da su ana cin mutuncin masu mutunci. To, duk wannan ya kamata al’umma ta fito ta yi maganinsu ta hanyar ƙin zaɓarsu, idan aka yi haka za a samu sauƙi sosai ko kuma a magance lamarin.” Kamar yadda ya bayyana.

LABARAI MASU NASABA

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

Siyasa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki

MASU ALAKA

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
Manyan Labarai

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Next Post
Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026
ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026
Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.