Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf da sanyin safiyar Asabar din nan ya fara rusa wasu gine-gine a filayen gwamnati da ake zargin gwamnatin Ganduje da cefanar da su.
![Abba Gida-Gida Wasu rukunin manyan gine-gine masu hawa 3 dauke da Shaguna 90 da Abba Gida-Gida ya rusa a Kano](https://hausa.leadership.ng/wp-content/uploads/2023/06/IMG-20230603-WA0019-768x576-1-300x225.jpg)
Yayin rusau din, an rusa wani gini mai hawa uku mai dauke da shaguna 90 da ke filin tseren Sukuwar dawaki, da ke Nasarawa da misalin karfe 2:00 na sare ranar Asabar nan.
Gwamnan wanda ya jagoranci aikin rusa ginin ya samu rakiyar kwamishinan ‘yan sanda Jihar, Muhammed Gumel.
![Abba Gida-Gida Abba Gida-Gida](https://hausa.leadership.ng/wp-content/uploads/2023/06/IMG-20230603-WA0023-768x346-1-300x135.jpg)
Idan dai za a iya tunawa Abba Kabir Yusuf, jim kadan bayan an rantsar da shi matsayin zababben gwamnan jihar Kano ya yi barazanar ruguza gine-gine a jihar kan kadarorin gwamnati da aka cefanar da su ga Jama’a.
Wannan dai shi ne rusau karo na farko da aka yi bayan hawansa mulki a ranar Litinin, 29 ga watan Mayu.
![Abba Gida-Gida Abba Gida-Gida](https://hausa.leadership.ng/wp-content/uploads/2023/06/IMG-20230603-WA0018-768x576-1-300x225.jpg)
Har ila yau, a ranar Juma’a, gwamnan ya umurci masu aikin gine-gine da ke gudanar da gine-gine a sansanin Alhazai na Kano da su dakata da aikin ginin da suke yi.