• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Barazanar Jami’an Tsaro Ana Ci Gaba Da Kone-konen Ofisoshin INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
‘Yansanda Sun Dakile Wani Hari A Ofishin INEC Dake Imo, Sun Kashe Maharan 3.
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da sanyin safiyar ranar Litinin ne wasu ‘yan bindiga suka kaddamar da hari a ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ke Owerri Babban Birnin Jihar Imo.

Harin ya yi sanadiyyar lalacewar wani bangaren ofishin bayan da nakiya ta fashe.
Kakakin rundunar ‘yansandar Jihar Imo, Mike Abbatam, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai ya bayyana cewa an samu nasarar kashe maharan guda uku tare da gano bama-bamai guda biyu.

  • Ba Za Mu Bari A Ci Gaba Da Kai Hare-hare Ga Ofisoshin INEC Ba, Cewar Sufeton ‘Yansanda

Wannan lamari ya faru ne cikin kwanaki takwas bayan kai farmaki a ofishin INEC da ke karamar hukumar Orlu a cikin jihar.
Wadanda ake zargin ‘yan daba ne sun kai irin wannan farmakin a ofisoshin INEC da ke jihohin Ebonyi da Osun da kuma Ogun a makonni hudun da suka gabata, lamarin da ya fara saka wa mutane shakku kan yuwuwar gudanar da zaben 2023.

Farmakin na Owerri ya gudana ne da misalin karfe uku na dare, inda jami’an tsaro suka samu nasarar harbe uku ciki har da kwamandansu har lahira. An dai samu nasarar kwato bindigogin kirar AK47 da wasu masu sarrafa kansu da motoci takwas daga hannun maharan.

Wata majiya ta ce, “A safiyar Lininin ce wasu ‘yan bindiga suka kaddamar da hari a ofishin INEC da ke Owerri a Jihar Imo, amma tawagar jami’an tsaro sun samu nasarar bude musu wuta tare da halaka uku ciki har da kwamandarsu.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

“An samu nasarar kwato motoci bakwai ciki har da bindigogin AK47 da masu sarrafa kansu. Mafi yawancin ‘yan bindigan sun gudu da raunikan harbi. Amma sai dai ‘yan daban sun kone motar ‘yansanda guda daya.”
Sai dai shi kuma Abbattam ya ce bindigogi kirar AK47 guda uku da motoci aka samu nasarar kwacewa.

Ya ce, “Mun kashe guda uku daga cikin maharan tare da kwato bindigogi kirar AK47 da masu sarrafa kansu muka samu nasarar kwatowa daga hannun maharan. Haka kuma mun kwato abubuwan fashewa guda biyu da motoci uku.”

An dai bayyana cewa an jibge jami’an tsaro a wasu yankuna da ke Owerri sakamakon wannan lamari.

Sakamakon kone-konen ofisoshin INEC a wasu sassan kasar nan, mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaron kasa (NSA), Majo Janar Babagana Monguno (rtd) da babban sufetan ‘yansanda na kasa, (IGP) Usman Baba Akali sun yi barazanar daukan mataki.

Dukkansu sun karanto laifukan da ke tattare da kone ofisoshin INEC, inda suka bayyana cewa an bai wa jamian tsaro umurnin kalubalantar duk wani mutum ko kungiya da ke kokarin kawo tsaiko kan zaben 2023.

Babban sufetan ‘yansanda ya bayyana cewa tuni ya umurci kwamishinonin ‘yansanda su samar da tsaro a dukkan ofisoshin INEC da ke jihohinsu.

A cewarsa, wannan aiki na wasu gurbatattun ‘yan siyasa ne da ke barazana ga zaben 2023.

Duk da wadannan zafafan hare-hare da ake kone-konen ofisoshin INEC, hukumar ta bayyana cewa ko kadan wannan ba zai iya hana gudanar da zaben 2023 ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Na Yi Bakin Kokarina A Matsayin Shugaban Nijeriya — Buhari

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

46 minutes ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

2 hours ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

3 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

7 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

15 hours ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

16 hours ago
Next Post
Goro

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.