• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Barazanar Jami’an Tsaro Ana Ci Gaba Da Kone-konen Ofisoshin INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
‘Yansanda Sun Dakile Wani Hari A Ofishin INEC Dake Imo, Sun Kashe Maharan 3.
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da sanyin safiyar ranar Litinin ne wasu ‘yan bindiga suka kaddamar da hari a ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ke Owerri Babban Birnin Jihar Imo.

Harin ya yi sanadiyyar lalacewar wani bangaren ofishin bayan da nakiya ta fashe.
Kakakin rundunar ‘yansandar Jihar Imo, Mike Abbatam, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai ya bayyana cewa an samu nasarar kashe maharan guda uku tare da gano bama-bamai guda biyu.

  • Ba Za Mu Bari A Ci Gaba Da Kai Hare-hare Ga Ofisoshin INEC Ba, Cewar Sufeton ‘Yansanda

Wannan lamari ya faru ne cikin kwanaki takwas bayan kai farmaki a ofishin INEC da ke karamar hukumar Orlu a cikin jihar.
Wadanda ake zargin ‘yan daba ne sun kai irin wannan farmakin a ofisoshin INEC da ke jihohin Ebonyi da Osun da kuma Ogun a makonni hudun da suka gabata, lamarin da ya fara saka wa mutane shakku kan yuwuwar gudanar da zaben 2023.

Farmakin na Owerri ya gudana ne da misalin karfe uku na dare, inda jami’an tsaro suka samu nasarar harbe uku ciki har da kwamandansu har lahira. An dai samu nasarar kwato bindigogin kirar AK47 da wasu masu sarrafa kansu da motoci takwas daga hannun maharan.

Wata majiya ta ce, “A safiyar Lininin ce wasu ‘yan bindiga suka kaddamar da hari a ofishin INEC da ke Owerri a Jihar Imo, amma tawagar jami’an tsaro sun samu nasarar bude musu wuta tare da halaka uku ciki har da kwamandarsu.

Labarai Masu Nasaba

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

“An samu nasarar kwato motoci bakwai ciki har da bindigogin AK47 da masu sarrafa kansu. Mafi yawancin ‘yan bindigan sun gudu da raunikan harbi. Amma sai dai ‘yan daban sun kone motar ‘yansanda guda daya.”
Sai dai shi kuma Abbattam ya ce bindigogi kirar AK47 guda uku da motoci aka samu nasarar kwacewa.

Ya ce, “Mun kashe guda uku daga cikin maharan tare da kwato bindigogi kirar AK47 da masu sarrafa kansu muka samu nasarar kwatowa daga hannun maharan. Haka kuma mun kwato abubuwan fashewa guda biyu da motoci uku.”

An dai bayyana cewa an jibge jami’an tsaro a wasu yankuna da ke Owerri sakamakon wannan lamari.

Sakamakon kone-konen ofisoshin INEC a wasu sassan kasar nan, mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaron kasa (NSA), Majo Janar Babagana Monguno (rtd) da babban sufetan ‘yansanda na kasa, (IGP) Usman Baba Akali sun yi barazanar daukan mataki.

Dukkansu sun karanto laifukan da ke tattare da kone ofisoshin INEC, inda suka bayyana cewa an bai wa jamian tsaro umurnin kalubalantar duk wani mutum ko kungiya da ke kokarin kawo tsaiko kan zaben 2023.

Babban sufetan ‘yansanda ya bayyana cewa tuni ya umurci kwamishinonin ‘yansanda su samar da tsaro a dukkan ofisoshin INEC da ke jihohinsu.

A cewarsa, wannan aiki na wasu gurbatattun ‘yan siyasa ne da ke barazana ga zaben 2023.

Duk da wadannan zafafan hare-hare da ake kone-konen ofisoshin INEC, hukumar ta bayyana cewa ko kadan wannan ba zai iya hana gudanar da zaben 2023 ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Na Yi Bakin Kokarina A Matsayin Shugaban Nijeriya — Buhari

Next Post

GORON JUMA’A

Related

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom
Labarai

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

2 hours ago
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Manyan Labarai

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

3 hours ago
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

12 hours ago
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

13 hours ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

16 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Da ɗumi-ɗuminsa

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

18 hours ago
Next Post
Goro

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC

Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC

July 29, 2025
EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

July 29, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

July 29, 2025
An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.