Shekaru biyu bayan da Shugaban kasa Bola Tinubu ya dauki matsaya a watan Mayun 2023 na dakatar da biyan tallafin man Fetur, gwamnatin tarayya ta samu damar tara rarar zunzurutun kudade har naira tiriliyan bakwai, amma tsananin rayuwa da yunwa na ci gaba da addabar ‘yan Nijeriya da kuma kananan kasuwanci.
Kananan sana’o’i wadanda tun da can suna ta faman fadi-tashi ta yadda za su ci gaba da gudanuwar da harkokinsu, maimakon sauyi sai kara koma-baya ake samu, lamarin da ya tilasta wa wasu da dama rufe harkokin sana’o’in nasu, don haka an kara samun marasa ayyukan yi a cikin kasar nan.
- Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600
- Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutane 3, Ta Wanke Gonakin Shinkafa Sama Da Hekta 10,000 A Neja
Masu ruwa da tsaki dai sun yi gargadin cewa ci gaba da samun tsadar kudin sufuri da na kudaden sarrafa kayayyaki su ne ke janyo tashin kudaden kayan bukatun yau da kullum, inda kuma gwamanti ce ke da alhakin dinke bakin zaren na tashin farashin kayayyakin masarufi.
Masu nazarin lamura sun yi kira da a farfado da lamarin tara kudaden shiga na jihohi, ciki har da neman zamanantar da tsarin tattara kudaden haraji, sanya dabaru wajen kyautata kudin shiga, tabbatar da ana biyan kudaden domin karfafa yanayin kudin jihohi da kuma tabbatar da cewa kudaden da jihohi ke amsa daga asusun hadaka na gwamantin tarayya ana amfani da su yadda ya dace.
Duk da kashe dala biliyan 2.9 wajen gyaran matatun man, kamfanin kula da albarkatun man fetur na kasa (NNPC) ya gaza farfado da matatun man gwamnati, abin da ya sa kasar har yanzu ta dogara da shigo da man fetur sama da kashi 60 cikin 100 daga kasashen waje da take sha a kullum.
Wani masanin tattalin arziki, Ademola Adigun, ya ce, duk da janye tallafin mai, sashin mai a Nijeriya ba ya tafiya kan ka’ida.
Ya yi bayanin cewa kawai an rage biyan tallafin ne amma ba wai an daina biya gaba daya ba, kuma babu gasa tsakanin ‘yan kasuwa wanda shi ma na haifar da nakasu.
Adigun ya soki tsarin sayar da danyen mai a kan kudin naira domin zabar da masu saye, ta yadda za a samar da lamari kamar na ‘ya’yan mowa da bora, da ke iya korar ‘yan kasuwa masu zaman kansu, lamarin da ya tilasta wa kusan gidajen mai 5,000 rufewa.
Adigun, duk da ya nuna farin ciki kan yadda masu zuba hannun jari suke nuna sha’awar zuba jari a sashin gas da yaba wa kan farfado da yanayin kasafin kudi, sai dai ya yi gargadin cewa har yanzu kasuwannin Nijeriya ba su da karfin janyo hankalin dandazon masu zuba jari.
Don haka ne ya yi kira da a samar da sauyi kan hanyoyin sufuri domin rage kudaden kayayyaki, ya ce, yawan kudin sufuri ne shi ne babban dalilin da ke janyo tashin farashin kayayyakin masarufi a kasar nan.
Shugaban PETROAN, Dakta Billy Gillis-Harry, ya ce, gwamnati ta kasa fito da abubuwan da ake sa rai ko ake tsammani da kuma cikakken tsari kan cire tallafin mai.
Ya koka kan matsalolin da har yanzu ake ci gaba da samu kan sauran matatun mai na gwamnatin tarayya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp