• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

by Khalid Idris Doya
1 day ago
in Manyan Labarai
0
Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shekaru biyu bayan da Shugaban kasa Bola Tinubu ya dauki matsaya a watan Mayun 2023 na dakatar da biyan tallafin man Fetur, gwamnatin tarayya ta samu damar tara rarar zunzurutun kudade har naira tiriliyan bakwai, amma tsananin rayuwa da yunwa na ci gaba da addabar ‘yan Nijeriya da kuma kananan kasuwanci. 

Kananan sana’o’i wadanda tun da can suna ta faman fadi-tashi ta yadda za su ci gaba da gudanuwar da harkokinsu, maimakon sauyi sai kara koma-baya ake samu, lamarin da ya tilasta wa wasu da dama rufe harkokin sana’o’in nasu, don haka an kara samun marasa ayyukan yi a cikin kasar nan.  

  • Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600
  • Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutane 3, Ta Wanke Gonakin Shinkafa Sama Da Hekta 10,000 A Neja

Masu ruwa da tsaki dai sun yi gargadin cewa ci gaba da samun tsadar kudin sufuri da na kudaden sarrafa kayayyaki su ne ke janyo tashin kudaden kayan bukatun yau da kullum, inda kuma gwamanti ce ke da alhakin dinke bakin zaren na tashin farashin kayayyakin masarufi.

Masu nazarin lamura sun yi kira da a farfado da lamarin tara kudaden shiga na jihohi, ciki har da neman zamanantar da tsarin tattara kudaden haraji, sanya dabaru wajen kyautata kudin shiga, tabbatar da ana biyan kudaden domin karfafa yanayin kudin jihohi da kuma tabbatar da cewa kudaden da jihohi ke amsa daga asusun hadaka na gwamantin tarayya ana amfani da su yadda ya dace. 

Duk da kashe dala biliyan 2.9 wajen gyaran matatun man, kamfanin kula da albarkatun man fetur na kasa (NNPC) ya gaza farfado da matatun man gwamnati, abin da ya sa kasar har yanzu ta dogara da shigo da man fetur sama da kashi 60 cikin 100 daga kasashen waje da take sha a kullum.

Labarai Masu Nasaba

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

Wani masanin tattalin arziki, Ademola Adigun, ya ce, duk da janye tallafin mai, sashin mai a Nijeriya ba ya tafiya kan ka’ida.

Ya yi bayanin cewa kawai an rage biyan tallafin ne amma ba wai an daina biya gaba daya ba, kuma babu gasa tsakanin ‘yan kasuwa wanda shi ma na haifar da nakasu. 

Adigun ya soki tsarin sayar da danyen mai a kan kudin naira domin zabar da masu saye, ta yadda za a samar da lamari kamar na ‘ya’yan mowa da bora, da ke iya korar ‘yan kasuwa masu zaman kansu, lamarin da ya tilasta wa kusan gidajen mai 5,000 rufewa.     

Adigun, duk da ya nuna farin ciki kan yadda masu zuba hannun jari suke nuna sha’awar zuba jari a sashin gas da yaba wa kan farfado da yanayin kasafin kudi, sai dai ya yi gargadin cewa har yanzu kasuwannin Nijeriya ba su da karfin janyo hankalin dandazon masu zuba jari.

Don haka ne ya yi kira da a samar da sauyi kan hanyoyin sufuri domin rage kudaden kayayyaki, ya ce, yawan kudin sufuri ne shi ne babban dalilin da ke janyo tashin farashin kayayyakin masarufi a kasar nan.

Shugaban PETROAN, Dakta Billy Gillis-Harry, ya ce, gwamnati ta kasa fito da abubuwan da ake sa rai ko ake tsammani da kuma cikakken tsari kan cire tallafin mai. 

Ya koka kan matsalolin da har yanzu ake ci gaba da samu kan sauran matatun mai na gwamnatin tarayya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FeturTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

Next Post

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)

Related

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

10 minutes ago
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

24 hours ago
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano
Manyan Labarai

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

1 day ago
Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa
Manyan Labarai

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

1 day ago
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

2 days ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

2 days ago
Next Post
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)

LABARAI MASU NASABA

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

May 31, 2025
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

May 31, 2025
Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115

May 31, 2025
Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

May 31, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa A Neja

May 31, 2025
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

May 31, 2025
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

May 31, 2025
Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa

Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa

May 31, 2025
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

May 31, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.