• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Matsalolin Da Ake Ciki, Nijeriya Za Ta Ci Gaba Da Bunƙasa – Minista

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa Nijeriya za ta ci gaba da bunƙasa duk da matsalolin da ta ke fuskanta.

A cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Abuja a ranar Lahadi, ministan ya ce, “Ba za a ce ba a cikin wani yanayi na matsi ba: akwai hauhawar farashi ga kayayyakin masarufin rayuwa da kuma barazana ga halin tsaro a wasu sassa na ƙasar nan.

  • Yaƙin Sudan: Gwamnatin Jigawa Ta Samarwa Dalibanta 194 Guraben Karatu A Jami’o’in Cyprus Da indiya
  • Gwamna Yusuf Na Neman Amincewar Majalisa Don Kafa Cibiyar Yaƙi Da Cututtuka Ta Kano

“Mu na da cikakkiyar masaniyar haƙƙin kulawa da ya rataya a wuyan Gwamnatin Tarayya ga kowane ɗan Nijeriya ba tare da la’akari da shekaru, jinsi, addini, ƙabila ko matsayinsa a al’umma ba.

 

“A ɓangaren tsaro, ana tunkarar duk wata barazana. Mu na kai hari kai-tsaye ga sansanonin ɓarayi, tare da cimma kyawawan nasarori. A makon jiya, an kashe ko an kama ɗimbin ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane da kuma ‘yan ta’adda.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

 

“Rikicin da ya sake kunno kai a Jihar Filato, a gaskiya abin baƙin ciki ne, amma mu na tabbatarwa kowa da kowa cewa, ana gurfanar da duk masu jawo fitina a sassan ƙasar nan a kotu. Za a yi masu shari’a, kuma za a dawo da zaman lafiya a dukkan wuraren da abin ya shafa.

 

“Mu na yaba wa namijin ƙoƙarin da hukumomin tsaro da masu farin kaya ke yi, waɗanda ba su yi sanyi a gwiwa ba don tabbatar da cewa mun samu natsuwa a gidajenmu da kan titunanmu, sannan masu aikata laifi ba su samu sauƙi ba.

 

“Dangane da tattalin arziki, dukkan ma’aikatu da hukumomin Gwamnatin Tarayya da abin ya shafa su na aiki tare da juna domin su rage tashin farashi, su daidaita tsarin canjin kuɗin ƙasar waje, kuma su samar da yanayi mai kyau don haɓaka harkar kasuwanci da zuba jari. Irin Nijeriyar da Shugaba Tinubu ya ke ƙoƙarin ginawa ita ce wadda ba a bar kowa a baya ba.

 

“Ana ta fito da tsare-tsare masu tasiri, waɗanda su ka haɗa da Shirin Bada Rance Ga Ɗalibai, shirin Shugaban Ƙasa na samar da motocin haya na CNG masu aiki da lantarki domin rage dogaro da fetur da man dizel, da sauran tsare-tsaren bada lamuni domin kasuwanci. Shirin samar da motocin zai rage tsadar kuɗin shiga motar haya da sama da kashi 50 cikin ɗari.

 

“Mu na kira ga ‘yan Nijeriya da su yi amfani da waɗannan damarmakin da zarar an fito da su, domin an yi su ne saboda kowa ya amfana.

 

“A daidai lokacin da mu ke tunkarar matsalolin mu haiƙan, ya kamata mu tuna wa dukkan ‘yan Nijeriya da su guji sauraren duk wasu muggan labarai da kalamai na ƙarya da ke jawo rarrabuwar kai. Misali, ba gaskiya ba ne cewar za a mayar da hedikwatar Hukumar Tashoshin Jiragen Sama ta Tarayya ta Nijeriya (FAAN) da wasu sassan Babban Bankin Nijeriya (CBN) zuwa Legas saboda dalilai na siyasa domin a ware wani sashe na ƙasar nan. Waɗannan zarge-zargen ba su da wata makama. Maimakon haka, waɗannan matakai ne da su ka shafi gudanarwa domin a inganta harkar aiki da rage kashe kuɗi.

 

“Ina kira ga dukkan ‘yan Nijeriya da su kula da duk wasu mutane da ƙungiyoyi a gida da ƙasar waje waɗanda su ka ƙware wajen yaɗa labaran bogi a gidajen rediyo da talabijin da soshiyal midiya, sannan su na yaɗa guntayen bidiyo da hotuna da aka sauya wa fasali don sakawa a intanet.

 

“A matsayin wani ɓangare na samar da amintaka a tsakanin ‘yan Nijeriya, za a ci gaba da yaƙin nan kan cin hanci da rashawa, kuma za a zurfafa shi. Don tabbatar da cewa babu wani ɗan lele, kuma an yi amfani da dukiyar jama’a wajen yi wa jama’a aiki, Shugaba Tinubu ya na sama wa hukumomin yaƙi da cin hanci dukkan goyon bayan da su ke buƙata domin gudanar da aikin su.

 

“Ba za mu cimma nasarar gina irin Nijeriyar da mu ke so ba idan har mu ka kafe kan kallon ƙalubalenmu da matsalolinmu kaɗai, ba ɗimbin damarmaki da kyawawan labarai da ke zagaye da mu ba. A sane mu ke cewa ƙasar na ci gaba da samun burin zuba jari daga ‘yan kasuwa na gida da na waje.

 

“Kada mu manta da ainihin abin da yake dahir: wato maimakon rarrabuwar kai da gaba da juna, za mu iya zama tare kuma mu bunƙasa cikin haɗin kai da fata tagari, tare da tabbacin cewa duk da waɗannan matsalolin masu wucewa da koma-baya da ake samu daga lokaci zuwa lokaci, babbar nasara ta na gab da zuwa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci gaban NijeriyaGwamnatin TinubuMinistan Yaɗa Labarai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Yi Nasarar Kirkirar Kwayar Halittar Nau’ikan Shanun Xizang Dake Bakin Karewa

Next Post

Sharhi: Shin Isra’Ila Za Ta Yi Biyayya Ga Hukuncin Kotun Duniya Game Da Yakin Gaza?

Related

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano
Labarai

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

2 hours ago
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

5 hours ago
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Labarai

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

6 hours ago
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe
Labarai

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

7 hours ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

9 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

10 hours ago
Next Post
Sharhi: Shin Isra’Ila Za Ta Yi Biyayya Ga Hukuncin Kotun Duniya Game Da Yakin Gaza?

Sharhi: Shin Isra’Ila Za Ta Yi Biyayya Ga Hukuncin Kotun Duniya Game Da Yakin Gaza?

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

August 13, 2025
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

August 13, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

August 13, 2025
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

August 13, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.