• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Na Fatan Alakar Sin Da Amurka Za Ta Inganta A Sabuwar Shekarar 2024

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Duniya Na Fatan Alakar Sin Da Amurka Za Ta Inganta A Sabuwar Shekarar 2024
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da jama’a a sassa daban-daban na duniya ke murnar shiga sabuwar shekara ta 2024, su ma shugabannin kasashen Sin da Amurka sun yi musayar sakon taya juna murnar cika shekaru 45 da kulla huldar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu.

A cikin sakonsa, shugaban kasar Sin Xi ya ce, kulla huldar diplomasiyya tsakanin Sin da Amurka, wani babban al’amari ne a tarihin alakar dake tsakanin kasashen biyu da ma na kasa da kasa.

  • Harbin Kasar Sin Ya Samu Bunkasuwar Yawon Shakatawa A Lokacin Hutun Murnar Sabuwar Shekara
  • Jawabin Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Game Da Cika Shekaru 45 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Amurka

Sanin kowa ne cewa, a cikin shekaru 45 da suka gabata, alakar kasashen biyu ta fuskanci wasu ’yan matsaloli, saboda nuna fuska biyu da bangaren Amurka ke yi, da yadda a wasu lokuta yake rashin cika alkawarun da ya dauka kan hadin gwiwar kasashen biyu, ko tsoma baki a harkokin cikin gidan kasar Sin ta hanyar fakewa ko dai da batun tsaro ko demokuradiya ko kakkabawa kamfanoni da ma daidaikun Sinawa takunkumai na kashin kai, wadanda a mafi yawan lokuta sun sabawa dokoki da yarjejeniyoyin hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu da ma na kasa da kasa, amma dai baki daya ana iya cewa, alakar ta ci gaba, wanda ba wai kawai ta kyautata jin dadin jama’ar kasashen biyu ba, har ma ta inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali da wadata a duk duniya.

Tarihi ya riga ya tabbatar kuma zai ci gaba da tabbatar da cewa, mutunta juna, zaman lafiya da hadin gwiwa da samun moriyar juna, ita ce hanyar da ta dace kasashen Sin da Amurka su daidaita da juna, a matsayinsu na manyan kasashe biyu. Kuma ya kamata ta zama alkiblar kokarin inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu a sabon zamani.

Kasar Sin ta sha bayyanawa cewa, a shirye take ta yi aiki tare da bangaren Amurka, don ci gaba da tafiyar da dangantakar kasashen biyu, ta yadda hakan zai amfanar da kasashen biyu da jama’arsu, da kuma sa kaimi ga zaman lafiya da ci gaban duniya baki daya. Don haka, ya dace bangaren na Amurka ya rika aiwatar da abubuwan da ya fada a zahiri ba wai maganar fatar baki ba. Mu gani a kasa, wai ana biki a gidansu kare.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

A cikin tasa wasikar taya murna, shugaba Biden ya ce, tun lokacin da aka kulla huldar diplomasiyya a shekarar 1979, dangantakar dake tsakanin Amurka da Sin, ta samar da wadata da damammaki a kasashen Amurka, da Sin da ma duniya baki daya.

A wannan karon ya ce, yana fatan dorawa kan ci gaba da magabatansa suka samu, da dimbin tarurruka da tattaunawar da ya yi da shugaba Xi, don ci gaba da inganta dangantakar dake tsakanin Amurka da Sin. Fatanmu dai shi ne, jagororin Amurka, za su rika aiwatar da dukkan abubuwan da suka fada a zahiri. A fada a cika, shi ne dattaku. Yanzu dai mun yi ban-kwana da shekarar 2023, muna fatan kasashen duniya za su rika kyautata alakar dake tsakaninsu a asabuwar shekarar 2024, ta yadda za mu gina duniya mai zaman lafiya da kwanciyar hankali da wadata, wadda kowa da kowa zai ji dadin zama a cikinta. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaAmurkaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masarautar Zazzau Za Ta Yi Nadin Sabon Magajin Gari

Next Post

Kakakin MOFA: Abin Da Duniya Ke Bukata Shi Ne Hadin Kai

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

9 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

10 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

12 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

13 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

20 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

22 hours ago
Next Post
Kakakin MOFA: Abin Da Duniya Ke Bukata Shi Ne Hadin Kai

Kakakin MOFA: Abin Da Duniya Ke Bukata Shi Ne Hadin Kai

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.