• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Na Fatan Alakar Sin Da Amurka Za Ta Inganta A Sabuwar Shekarar 2024

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Duniya Na Fatan Alakar Sin Da Amurka Za Ta Inganta A Sabuwar Shekarar 2024
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da jama’a a sassa daban-daban na duniya ke murnar shiga sabuwar shekara ta 2024, su ma shugabannin kasashen Sin da Amurka sun yi musayar sakon taya juna murnar cika shekaru 45 da kulla huldar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu.

A cikin sakonsa, shugaban kasar Sin Xi ya ce, kulla huldar diplomasiyya tsakanin Sin da Amurka, wani babban al’amari ne a tarihin alakar dake tsakanin kasashen biyu da ma na kasa da kasa.

  • Harbin Kasar Sin Ya Samu Bunkasuwar Yawon Shakatawa A Lokacin Hutun Murnar Sabuwar Shekara
  • Jawabin Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Sin Game Da Cika Shekaru 45 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Amurka

Sanin kowa ne cewa, a cikin shekaru 45 da suka gabata, alakar kasashen biyu ta fuskanci wasu ’yan matsaloli, saboda nuna fuska biyu da bangaren Amurka ke yi, da yadda a wasu lokuta yake rashin cika alkawarun da ya dauka kan hadin gwiwar kasashen biyu, ko tsoma baki a harkokin cikin gidan kasar Sin ta hanyar fakewa ko dai da batun tsaro ko demokuradiya ko kakkabawa kamfanoni da ma daidaikun Sinawa takunkumai na kashin kai, wadanda a mafi yawan lokuta sun sabawa dokoki da yarjejeniyoyin hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu da ma na kasa da kasa, amma dai baki daya ana iya cewa, alakar ta ci gaba, wanda ba wai kawai ta kyautata jin dadin jama’ar kasashen biyu ba, har ma ta inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali da wadata a duk duniya.

Tarihi ya riga ya tabbatar kuma zai ci gaba da tabbatar da cewa, mutunta juna, zaman lafiya da hadin gwiwa da samun moriyar juna, ita ce hanyar da ta dace kasashen Sin da Amurka su daidaita da juna, a matsayinsu na manyan kasashe biyu. Kuma ya kamata ta zama alkiblar kokarin inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu a sabon zamani.

Kasar Sin ta sha bayyanawa cewa, a shirye take ta yi aiki tare da bangaren Amurka, don ci gaba da tafiyar da dangantakar kasashen biyu, ta yadda hakan zai amfanar da kasashen biyu da jama’arsu, da kuma sa kaimi ga zaman lafiya da ci gaban duniya baki daya. Don haka, ya dace bangaren na Amurka ya rika aiwatar da abubuwan da ya fada a zahiri ba wai maganar fatar baki ba. Mu gani a kasa, wai ana biki a gidansu kare.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

A cikin tasa wasikar taya murna, shugaba Biden ya ce, tun lokacin da aka kulla huldar diplomasiyya a shekarar 1979, dangantakar dake tsakanin Amurka da Sin, ta samar da wadata da damammaki a kasashen Amurka, da Sin da ma duniya baki daya.

A wannan karon ya ce, yana fatan dorawa kan ci gaba da magabatansa suka samu, da dimbin tarurruka da tattaunawar da ya yi da shugaba Xi, don ci gaba da inganta dangantakar dake tsakanin Amurka da Sin. Fatanmu dai shi ne, jagororin Amurka, za su rika aiwatar da dukkan abubuwan da suka fada a zahiri. A fada a cika, shi ne dattaku. Yanzu dai mun yi ban-kwana da shekarar 2023, muna fatan kasashen duniya za su rika kyautata alakar dake tsakaninsu a asabuwar shekarar 2024, ta yadda za mu gina duniya mai zaman lafiya da kwanciyar hankali da wadata, wadda kowa da kowa zai ji dadin zama a cikinta. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaAmurkaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masarautar Zazzau Za Ta Yi Nadin Sabon Magajin Gari

Next Post

Kakakin MOFA: Abin Da Duniya Ke Bukata Shi Ne Hadin Kai

Related

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli
Daga Birnin Sin

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

5 hours ago
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

7 hours ago
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13
Daga Birnin Sin

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

8 hours ago
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka
Daga Birnin Sin

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

8 hours ago
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya
Daga Birnin Sin

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

9 hours ago
Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

10 hours ago
Next Post
Kakakin MOFA: Abin Da Duniya Ke Bukata Shi Ne Hadin Kai

Kakakin MOFA: Abin Da Duniya Ke Bukata Shi Ne Hadin Kai

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.