• English
  • Business News
Tuesday, June 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Na Fatan Samun Karin Kadarori Masu Daraja Irin “Ziri Daya Da Hanya Daya”

by Sulaiman
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ziri Daya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda muke gani a zahiri, kasar Sin ta samarwa duniya gudummawar tsarin ci gaba cikin sauri tsakanin shekaru 10 da suka gabata, ta hanyar gabatar da shawarar “Ziri daya da hanya daya” ko BRI. Cikin manyan nasarorin da wannan shawara ta samar akwai cike gibin zuba jari a fannin samar da manyan ababen more rayuwa tsakanin kasashe masu ci gaba da masu tasowa.

Kafin kaddamar da wannan shawara ta BRI, duniya musamman kasashe masu tasowa na da matukar burin samun masu zuba jari, to sai dai kuma cibiyoyin hada-hadar kudi da suka saba cudanya da su, ko dai ba za su iya ba, ko kuma ba su da niyyar yin hakan. Ana cikin wannan yanayi ne kuma, kasar Sin ta gabatar da shawarar BRI, wadda ta samu matukar karbuwa tsakanin kasashen duniya, musamman masu tasowa da masu rauni sosai.

  • Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Uruguay
  • Messi Da Ronado Za Su Hadu A Wani Wasan Sada Zumunci A Watan Fabrairu

Sai dai wani abun lura a nan shi ne yadda wannan shawara mai matukar tasiri ga samar da ci gaba, ke ta shan suka tun kafuwarta kawo yanzu. Tabbas abun takaici ne ganin yadda wasu ’yan siyasar yammacin duniya suka dage sai sun shafawa shawarar BRI kashin kaji ta hanyar kitsa karairai, da sharri iri-iri. Har ma wasu na kiran ta da “tarkon bashi”, ko “shirin tsoma hannu cikin harkokin cikin gidan wasu kasashe”, ko ma “sabon salon mulkin mallaka” da dai sauransu.

Har ila yau, cikin irin wadannan ’yan siyasa da masu goya musu baya cikin jagororin wasu sassa, akwai masu amfani da kalmar dimokaradiyya a matsayin makami. Inda har kullum suke sukar tsarin dimokaradiyyar kasar Sin, da salon jagorancin al’ummarta, duk da cewa abu ne a zahiri, salon mulkin kasar Sin ya yi nasarar ciyar da kasar gaba, ya kuma ba da damar tsame miliyoyin al’ummar Sinawa daga kangin talauci, har ma kasar ta kai ga shiga sahun kasashe masu daidaitaccen tsarin tattalin arziki, kuma wuri da masu zuba jari ke rububin shiga.

Ko shakka babu, la’akari da wadannan dalilai, za mu gane cewa, sama da ko wane lokaci a tarihi, a yanzu duniya ta fi bukatar kadarori irin shawarar BRI, domin tabbatar da kyautatuwar rayuwar bil Adama, sabanin duk wata farfaganda maras tushe, wadda ba za ta amfani kowa ba, sai ma dai ruwa wutar rashin jituwa, da nunawa juna yatsa, da haifar da fito-na-fito.

Labarai Masu Nasaba

Wang Yi Ya Gabatar Da Jawabi Albarkacin “Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa” Karo Na Farko Na MDD

Sin Da Kenya Sun Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Kiwon Lafiya

Karin karbuwa da shawarar BRI ke samu tsakanin sassan kasa da kasa, ya nuna yadda al’ummun duniya ke kara maraba da sabon salo, kuma sabuwar turbar ci gaba, da ma kyakkyawar alkiblar da duniya ke fuskanta.

Duniya ta rungumi ci gaba tare, da warware matsalolin bil Adama cikin hadin gwiwa, maimakon kara bullo da wasu sabbin matsaloli. Don haka shawara ga sassan ’yan siyasar yammacin duniya, ita ce su rungumi hadin gwiwa da dukkanin sassa, domin cimma fa’ida ga kowa. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: SinTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukuncin Zaben Nasarawa: PDP Za Ta Daukaka Kara Zuwa Kotun Koli

Next Post

An Bude Taron Baje Kolin Hakkin Mallakar Fasaha Karo Na 9 A Chengdu

Related

Wang Yi Ya Gabatar Da Jawabi Albarkacin “Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa” Karo Na Farko Na MDD
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gabatar Da Jawabi Albarkacin “Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa” Karo Na Farko Na MDD

42 minutes ago
Sin Da Kenya Sun Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Kiwon Lafiya
Daga Birnin Sin

Sin Da Kenya Sun Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Kiwon Lafiya

47 minutes ago
Xi Ya Zanta Da Takwaransa Na Kasar Koriya Ta Kudu  
Daga Birnin Sin

Xi Ya Zanta Da Takwaransa Na Kasar Koriya Ta Kudu  

3 hours ago
Kyakkyawar Hulda Tsakanin Sin Da Koriya Ta Kudu Na Da Muhimmanci Ga Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankinsu
Daga Birnin Sin

Kyakkyawar Hulda Tsakanin Sin Da Koriya Ta Kudu Na Da Muhimmanci Ga Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankinsu

4 hours ago
Sin Na Maraba Da Karin ‘Yan Kasuwar Ketare Dake Son Gudanar Da Hada-hada Don Cimma Moriyar Juna
Daga Birnin Sin

Sin Na Maraba Da Karin ‘Yan Kasuwar Ketare Dake Son Gudanar Da Hada-hada Don Cimma Moriyar Juna

4 hours ago
Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Babban Taron MDD Kan Tekuna
Daga Birnin Sin

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Babban Taron MDD Kan Tekuna

6 hours ago
Next Post
Chengdu

An Bude Taron Baje Kolin Hakkin Mallakar Fasaha Karo Na 9 A Chengdu

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Ya Gabatar Da Jawabi Albarkacin “Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa” Karo Na Farko Na MDD

Wang Yi Ya Gabatar Da Jawabi Albarkacin “Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa” Karo Na Farko Na MDD

June 10, 2025
Sin Da Kenya Sun Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Kiwon Lafiya

Sin Da Kenya Sun Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Kiwon Lafiya

June 10, 2025
Rashin Tsaro: Gwamnatin Kogi Ta Gargadi Siyasantar Da Kalubalen Tsaro A Jihar

Rashin Tsaro: Gwamnatin Kogi Ta Gargadi Siyasantar Da Kalubalen Tsaro A Jihar

June 10, 2025
Xi Ya Zanta Da Takwaransa Na Kasar Koriya Ta Kudu  

Xi Ya Zanta Da Takwaransa Na Kasar Koriya Ta Kudu  

June 10, 2025
Kyakkyawar Hulda Tsakanin Sin Da Koriya Ta Kudu Na Da Muhimmanci Ga Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankinsu

Kyakkyawar Hulda Tsakanin Sin Da Koriya Ta Kudu Na Da Muhimmanci Ga Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankinsu

June 10, 2025
Sin Na Maraba Da Karin ‘Yan Kasuwar Ketare Dake Son Gudanar Da Hada-hada Don Cimma Moriyar Juna

Sin Na Maraba Da Karin ‘Yan Kasuwar Ketare Dake Son Gudanar Da Hada-hada Don Cimma Moriyar Juna

June 10, 2025
Gwamna Zulum Ya Bayar Da Tallafin Miliyan 300 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Mokwa

Gwamna Zulum Ya Bayar Da Tallafin Miliyan 300 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Mokwa

June 10, 2025
Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Babban Taron MDD Kan Tekuna

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Babban Taron MDD Kan Tekuna

June 10, 2025
Mutum 10 Sun Mutu Sakamakon Harbe-harbe A Makarantar Sakandire A Kasar Austriya

Mutum 10 Sun Mutu Sakamakon Harbe-harbe A Makarantar Sakandire A Kasar Austriya

June 10, 2025
Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

June 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.