• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Na Jimamin Jiang Zemin

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Duniya Na Jimamin Jiang Zemin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da tsakar ranar Laraba 30 ga watan Nuwanban shekarar 2022 ne, kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin (JKS), da zaunannen kwamitin majalissar wakilan jama’ar kasar Sin, da majalissar gudanarwar kasar, da kwamitin majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar, da hukumar kolin rundunar sojoji ta JKS da jamhuriyar jama’ar kasar Sin suka tabbatar da rasuwar tsohon babban sakataren kwamitin kolin JKS, kana tsohon shugaban kasar Sin Jiang Zemin.

A yayin cikakken zama karo na 4 na kwamitin kolin JKS na 13 da aka gudanar a watan Yunin shekarar 1989, an zabe shi a matsayin babban sakataren kwamitin kolin JKS. Ya rike wannan matsayi, daga watan Yunin shekarar 1989 zuwa watan Nuwamban shekarar 2002.

  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Isa Birnin Riyadh Kasar Saudiyya

Sannan a yayin babban taron jama’ar kasar Sin karo na 8 da aka gudanar a watan Maris na shekarar 1993, an zabe shi a matsayin shugaban kasar Sin. Ya zama shugaban kasar Sin a tsakanin watan Maris na shekarar 1993 zuwa watan Maris na shekarar 2003.

A lokacin da yake rike da mukamin shugaban kasar Sin, marigayi Jiang Zemin ya kai ziyarar aiki tarayyar Nijeriya a watan Afrilun shekarar 2002, domin kokarin bunkasa dangantaka da kuma sada zumunta tsakanin kasar Sin da Nijeriya.

An bayyana Jiang Zemin a matsayin jajirtaccen shugaba mai martaba, wanda dukkanin ’yan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin suka aminta da shi, wanda ya samu karbuwa daga rundunar sojojin kasar Sin, da daukacin al’ummar Sinawa, kana babban mabiyin akidar Markisanci, kuma babban masani a fannin siyasa da ayyukan soji da diflomasiyya, jarumin jam’iyyar kwaminis da ya taka rawar gani, kuma shugaba na-gari a tafarkin gurguzu mai halayyar musamman ta kasar Sin. Kaza lika marigayin jigo ne na jagororin kasar Sin na zuriya ta uku, wanda ya kafa ginshikin ka’idar mulki ta “wakilci a fannoni uku.

Labarai Masu Nasaba

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Tun lokacin har zuwa yanzu, shugabannin kasashe da kungiyoyin kasa da kasa da dama, suka aike da wasikun ta’aziya ga shugaban kasar Xi Jinping, inda suka nuna jimami game da rasuwar Jiang Zemin, inda suka bayyana shi a matsayin wanda ya ba da babbar gudummawa ga ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’ummar Sinawa da kyautata matsayinta a duniya, inganta dangantakar dake tsakanin Sin da kasashe daban-daban, kuma dan siyasa mai kima da fara’a, jagoran da ya tsaya tsayin daka domin ganin kasar Sin ta shiga cikin harkokin kasa da kasa, da shigar da kasar cikin kungiyar cinikayyar duniya, kana gwarzo da ya jagoranci Sin wajen karbar bakuncin babban taron mata na duniya karo na hudu dake da babbar ma’ana.

Sun kuma amince cewa, tsakanin karshen shekarun 1980 da farkon shekarun 1990, lokaci ne mai matukar muhimmanci ga makomar jam’iyyar ta kasar ta Sin, a lokacin marigayi Jiang Zemin ya jagoranci shugabannin kasar wajen cimma sabon ci gaba na aiwatar da sauye-sauye, da bude kofa a Sin, da ma zamanintar da kasar mai mulkin gurguzu.

Hakaki an yi rashin gwarzo, wanda duniya ta shaida gagarumin rawar da ya taka a lokuta daban-daban, wadanda suka kasance masu muhimmanci ba kawai ga kasar Sin ba, har ga duniya baki daya. Halin mutum aka ce jarinsa. Mariyagi Jiang Zemin ya mutu ne, yana da shekaru 96 a duniya. Ya kuma bar kyawawan halaye abin koyi. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

“Dalilanmu Na Cafke Fitaccen Mawaki D’banj” —ICPC

Next Post

Bagudu Ya Amince Da Karbar Bakuncin Gasar Musabakar Alkur’ani Ta Shekarar 2022 A Kebbi

Related

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

3 hours ago
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
Daga Birnin Sin

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

4 hours ago
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
Daga Birnin Sin

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

5 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

6 hours ago
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
Daga Birnin Sin

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

7 hours ago
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
Daga Birnin Sin

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

9 hours ago
Next Post
Bagudu Ya Amince Da Karbar Bakuncin Gasar Musabakar Alkur’ani Ta Shekarar 2022 A Kebbi

Bagudu Ya Amince Da Karbar Bakuncin Gasar Musabakar Alkur'ani Ta Shekarar 2022 A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.