• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Na Jimamin Jiang Zemin

by CMG Hausa
3 years ago
Jiang Zemin

Da tsakar ranar Laraba 30 ga watan Nuwanban shekarar 2022 ne, kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin (JKS), da zaunannen kwamitin majalissar wakilan jama’ar kasar Sin, da majalissar gudanarwar kasar, da kwamitin majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar, da hukumar kolin rundunar sojoji ta JKS da jamhuriyar jama’ar kasar Sin suka tabbatar da rasuwar tsohon babban sakataren kwamitin kolin JKS, kana tsohon shugaban kasar Sin Jiang Zemin.

A yayin cikakken zama karo na 4 na kwamitin kolin JKS na 13 da aka gudanar a watan Yunin shekarar 1989, an zabe shi a matsayin babban sakataren kwamitin kolin JKS. Ya rike wannan matsayi, daga watan Yunin shekarar 1989 zuwa watan Nuwamban shekarar 2002.

  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Isa Birnin Riyadh Kasar Saudiyya

Sannan a yayin babban taron jama’ar kasar Sin karo na 8 da aka gudanar a watan Maris na shekarar 1993, an zabe shi a matsayin shugaban kasar Sin. Ya zama shugaban kasar Sin a tsakanin watan Maris na shekarar 1993 zuwa watan Maris na shekarar 2003.

A lokacin da yake rike da mukamin shugaban kasar Sin, marigayi Jiang Zemin ya kai ziyarar aiki tarayyar Nijeriya a watan Afrilun shekarar 2002, domin kokarin bunkasa dangantaka da kuma sada zumunta tsakanin kasar Sin da Nijeriya.

An bayyana Jiang Zemin a matsayin jajirtaccen shugaba mai martaba, wanda dukkanin ’yan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin suka aminta da shi, wanda ya samu karbuwa daga rundunar sojojin kasar Sin, da daukacin al’ummar Sinawa, kana babban mabiyin akidar Markisanci, kuma babban masani a fannin siyasa da ayyukan soji da diflomasiyya, jarumin jam’iyyar kwaminis da ya taka rawar gani, kuma shugaba na-gari a tafarkin gurguzu mai halayyar musamman ta kasar Sin. Kaza lika marigayin jigo ne na jagororin kasar Sin na zuriya ta uku, wanda ya kafa ginshikin ka’idar mulki ta “wakilci a fannoni uku.

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Tun lokacin har zuwa yanzu, shugabannin kasashe da kungiyoyin kasa da kasa da dama, suka aike da wasikun ta’aziya ga shugaban kasar Xi Jinping, inda suka nuna jimami game da rasuwar Jiang Zemin, inda suka bayyana shi a matsayin wanda ya ba da babbar gudummawa ga ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’ummar Sinawa da kyautata matsayinta a duniya, inganta dangantakar dake tsakanin Sin da kasashe daban-daban, kuma dan siyasa mai kima da fara’a, jagoran da ya tsaya tsayin daka domin ganin kasar Sin ta shiga cikin harkokin kasa da kasa, da shigar da kasar cikin kungiyar cinikayyar duniya, kana gwarzo da ya jagoranci Sin wajen karbar bakuncin babban taron mata na duniya karo na hudu dake da babbar ma’ana.

Sun kuma amince cewa, tsakanin karshen shekarun 1980 da farkon shekarun 1990, lokaci ne mai matukar muhimmanci ga makomar jam’iyyar ta kasar ta Sin, a lokacin marigayi Jiang Zemin ya jagoranci shugabannin kasar wajen cimma sabon ci gaba na aiwatar da sauye-sauye, da bude kofa a Sin, da ma zamanintar da kasar mai mulkin gurguzu.

Hakaki an yi rashin gwarzo, wanda duniya ta shaida gagarumin rawar da ya taka a lokuta daban-daban, wadanda suka kasance masu muhimmanci ba kawai ga kasar Sin ba, har ga duniya baki daya. Halin mutum aka ce jarinsa. Mariyagi Jiang Zemin ya mutu ne, yana da shekaru 96 a duniya. Ya kuma bar kyawawan halaye abin koyi. (Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal
Daga Birnin Sin

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025
Daga Birnin Sin

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
Next Post
Bagudu Ya Amince Da Karbar Bakuncin Gasar Musabakar Alkur’ani Ta Shekarar 2022 A Kebbi

Bagudu Ya Amince Da Karbar Bakuncin Gasar Musabakar Alkur'ani Ta Shekarar 2022 A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.