ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Na Jimamin Jiang Zemin

by CMG Hausa
3 years ago
Jiang Zemin

Da tsakar ranar Laraba 30 ga watan Nuwanban shekarar 2022 ne, kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin (JKS), da zaunannen kwamitin majalissar wakilan jama’ar kasar Sin, da majalissar gudanarwar kasar, da kwamitin majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar, da hukumar kolin rundunar sojoji ta JKS da jamhuriyar jama’ar kasar Sin suka tabbatar da rasuwar tsohon babban sakataren kwamitin kolin JKS, kana tsohon shugaban kasar Sin Jiang Zemin.

A yayin cikakken zama karo na 4 na kwamitin kolin JKS na 13 da aka gudanar a watan Yunin shekarar 1989, an zabe shi a matsayin babban sakataren kwamitin kolin JKS. Ya rike wannan matsayi, daga watan Yunin shekarar 1989 zuwa watan Nuwamban shekarar 2002.

  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Isa Birnin Riyadh Kasar Saudiyya

Sannan a yayin babban taron jama’ar kasar Sin karo na 8 da aka gudanar a watan Maris na shekarar 1993, an zabe shi a matsayin shugaban kasar Sin. Ya zama shugaban kasar Sin a tsakanin watan Maris na shekarar 1993 zuwa watan Maris na shekarar 2003.

ADVERTISEMENT

A lokacin da yake rike da mukamin shugaban kasar Sin, marigayi Jiang Zemin ya kai ziyarar aiki tarayyar Nijeriya a watan Afrilun shekarar 2002, domin kokarin bunkasa dangantaka da kuma sada zumunta tsakanin kasar Sin da Nijeriya.

An bayyana Jiang Zemin a matsayin jajirtaccen shugaba mai martaba, wanda dukkanin ’yan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin suka aminta da shi, wanda ya samu karbuwa daga rundunar sojojin kasar Sin, da daukacin al’ummar Sinawa, kana babban mabiyin akidar Markisanci, kuma babban masani a fannin siyasa da ayyukan soji da diflomasiyya, jarumin jam’iyyar kwaminis da ya taka rawar gani, kuma shugaba na-gari a tafarkin gurguzu mai halayyar musamman ta kasar Sin. Kaza lika marigayin jigo ne na jagororin kasar Sin na zuriya ta uku, wanda ya kafa ginshikin ka’idar mulki ta “wakilci a fannoni uku.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Tun lokacin har zuwa yanzu, shugabannin kasashe da kungiyoyin kasa da kasa da dama, suka aike da wasikun ta’aziya ga shugaban kasar Xi Jinping, inda suka nuna jimami game da rasuwar Jiang Zemin, inda suka bayyana shi a matsayin wanda ya ba da babbar gudummawa ga ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’ummar Sinawa da kyautata matsayinta a duniya, inganta dangantakar dake tsakanin Sin da kasashe daban-daban, kuma dan siyasa mai kima da fara’a, jagoran da ya tsaya tsayin daka domin ganin kasar Sin ta shiga cikin harkokin kasa da kasa, da shigar da kasar cikin kungiyar cinikayyar duniya, kana gwarzo da ya jagoranci Sin wajen karbar bakuncin babban taron mata na duniya karo na hudu dake da babbar ma’ana.

Sun kuma amince cewa, tsakanin karshen shekarun 1980 da farkon shekarun 1990, lokaci ne mai matukar muhimmanci ga makomar jam’iyyar ta kasar ta Sin, a lokacin marigayi Jiang Zemin ya jagoranci shugabannin kasar wajen cimma sabon ci gaba na aiwatar da sauye-sauye, da bude kofa a Sin, da ma zamanintar da kasar mai mulkin gurguzu.

Hakaki an yi rashin gwarzo, wanda duniya ta shaida gagarumin rawar da ya taka a lokuta daban-daban, wadanda suka kasance masu muhimmanci ba kawai ga kasar Sin ba, har ga duniya baki daya. Halin mutum aka ce jarinsa. Mariyagi Jiang Zemin ya mutu ne, yana da shekaru 96 a duniya. Ya kuma bar kyawawan halaye abin koyi. (Ibrahim Yaya)

Jiang Zemin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Bagudu Ya Amince Da Karbar Bakuncin Gasar Musabakar Alkur’ani Ta Shekarar 2022 A Kebbi

Bagudu Ya Amince Da Karbar Bakuncin Gasar Musabakar Alkur'ani Ta Shekarar 2022 A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.