• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Ta Shiga Alhinin Mutuwar Sama Da Mutum 3,000 A Turkiyya Da Siriya

by Abubakar Abba
3 years ago
Turkiyya

Shugabannin Duniya na ci gaba da zaman makoki na mutane sama da 3,000 da suka mutu sakamakon girzizar kasa da ta auku a Turkiyya da kuma a Arewa Maso Gabashin Siriya.

Iftila’in ya kuma janyo dubban mutane da suka samu raunuka tare da raba su da mahuallansu, inda kuma ake ta kokarin kubutar da sauran mutanen da lamarin ya rutsa da su.

  • An Gurfanar Da ‘Yan Bangar Siyasa 10 A Gaban Kotu A Sakkwato 
  • NIS Ta Kwato Katin Zabe 106 Daga Hannun Bakin Haure A Kwara

Nauyin girgizar ya kai 7.8, inda kuma iftila’in ya kara haifar da matsala musamman ga miliyoyin ‘yan Siriya da ta shafe shekaru ta na fama da yaki.

Wani dan kasar Siriya Abdul Salam al-Mahmou, ya bayyana cewa, girgizar ta zo ne kamar tashin duniya, inda ya kara da cewa, ta taho ne sanyi sai kuma ruwan sama, akwai kuma bukatar a kubutar da rayuwar jama’a.

Sashen kula da binciken yanayi na Kasar Amurka ya ce, girgizar ta kasance mafi girma da aka taba samu a fadin duniya tun bayan wacce ta auku kudancin Atlantik.

LABARAI MASU NASABA

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

Ministan Lafiya na Turkiyya, Fahrettin Koca, ya sanar da cewa, yawan wadanda suka rasu a Turkiyya ya kai 1,651, inda kuma mutane 11,119 suka samu raunuka.

Bisa adadin da gwamnatin kasar Siriya ta fitar ta ce, akalla mutane 1,073 suka rasu.

Adadin wadanda suka samu raunuka a jiya litinin ya haura na girgizar kasar da aka yi a Turkiyya a 1999 shine mafi yawa.

Shugaban kasar Turkiyya Tayyip Erdogan, wanda ya ke tunkrar zabe mai zafi a watan mayu mai zuwa, ya danganta iftila’in a matsayin mafi muni akan wacce ta auku a 1939.

Har ila yau, Siriya da ta fuskanci yakin basasa da aka shafe shekaru 11 ana yi, ministan lafiya na kasar ya ce, an kashe mutane 593, inda kuma mutane 1,326 suka samu raunuka.

Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya nuna kaduwarsa akan iftila’in da ya auku a kasashen biyu, inda kuma ya yi alkawarin taimaka wa kasashen biyu.

Fafaroma na Vatican Pope Francis shi ma ya nuna alhininsa akan iftila’in da ya aukawa kasashen biyu.

Bugu da kari, gwamnatin Birtaniya ta ce za ta masu yin ceto da tawagar likitoci zuwa kasar Turkiyya.

Shi ma a na sa sakon na jajanta wa shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika sakon ta’aziyar sa ga kasashen biyu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar
Manyan Labarai

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai
Daga Birnin Sin

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Next Post
Zanga-Zanga Ta Barke A Ondo Kan Karancin Kudi Da Man Fetur

Zanga-Zanga Ta Barke A Ondo Kan Karancin Kudi Da Man Fetur

LABARAI MASU NASABA

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Turkiyya

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025
Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.