ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Ta Shiga Alhinin Mutuwar Sama Da Mutum 3,000 A Turkiyya Da Siriya

by Abubakar Abba
4 years ago
Turkiyya

Shugabannin Duniya na ci gaba da zaman makoki na mutane sama da 3,000 da suka mutu sakamakon girzizar kasa da ta auku a Turkiyya da kuma a Arewa Maso Gabashin Siriya.

Iftila’in ya kuma janyo dubban mutane da suka samu raunuka tare da raba su da mahuallansu, inda kuma ake ta kokarin kubutar da sauran mutanen da lamarin ya rutsa da su.

  • An Gurfanar Da ‘Yan Bangar Siyasa 10 A Gaban Kotu A Sakkwato 
  • NIS Ta Kwato Katin Zabe 106 Daga Hannun Bakin Haure A Kwara

Nauyin girgizar ya kai 7.8, inda kuma iftila’in ya kara haifar da matsala musamman ga miliyoyin ‘yan Siriya da ta shafe shekaru ta na fama da yaki.

ADVERTISEMENT

Wani dan kasar Siriya Abdul Salam al-Mahmou, ya bayyana cewa, girgizar ta zo ne kamar tashin duniya, inda ya kara da cewa, ta taho ne sanyi sai kuma ruwan sama, akwai kuma bukatar a kubutar da rayuwar jama’a.

Sashen kula da binciken yanayi na Kasar Amurka ya ce, girgizar ta kasance mafi girma da aka taba samu a fadin duniya tun bayan wacce ta auku kudancin Atlantik.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ministan Lafiya na Turkiyya, Fahrettin Koca, ya sanar da cewa, yawan wadanda suka rasu a Turkiyya ya kai 1,651, inda kuma mutane 11,119 suka samu raunuka.

Bisa adadin da gwamnatin kasar Siriya ta fitar ta ce, akalla mutane 1,073 suka rasu.

Adadin wadanda suka samu raunuka a jiya litinin ya haura na girgizar kasar da aka yi a Turkiyya a 1999 shine mafi yawa.

Shugaban kasar Turkiyya Tayyip Erdogan, wanda ya ke tunkrar zabe mai zafi a watan mayu mai zuwa, ya danganta iftila’in a matsayin mafi muni akan wacce ta auku a 1939.

Har ila yau, Siriya da ta fuskanci yakin basasa da aka shafe shekaru 11 ana yi, ministan lafiya na kasar ya ce, an kashe mutane 593, inda kuma mutane 1,326 suka samu raunuka.

Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya nuna kaduwarsa akan iftila’in da ya auku a kasashen biyu, inda kuma ya yi alkawarin taimaka wa kasashen biyu.

Fafaroma na Vatican Pope Francis shi ma ya nuna alhininsa akan iftila’in da ya aukawa kasashen biyu.

Bugu da kari, gwamnatin Birtaniya ta ce za ta masu yin ceto da tawagar likitoci zuwa kasar Turkiyya.

Shi ma a na sa sakon na jajanta wa shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika sakon ta’aziyar sa ga kasashen biyu.

Turkiyya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Next Post
Zanga-Zanga Ta Barke A Ondo Kan Karancin Kudi Da Man Fetur

Zanga-Zanga Ta Barke A Ondo Kan Karancin Kudi Da Man Fetur

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.