• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniyarmu Na Da Girman Da Ya Ishi Kasa Da Kasa Su Samu Ci Gaba Tare

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Duniyarmu Na Da Girman Da Ya Ishi Kasa Da Kasa Su Samu Ci Gaba Tare
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai wata kasar da ta kafa sansanonin soja kimanin 750 a ketare, wadanda suka barbazu a kasashe da shiyyoyi 80 na Asiya da Turai da gabas ta tsakiya da Afirka da Latin Amurka, matakin da ya sa ta zama kasar da ta fi yawan mallakar sansanonin soja a duniya. To, haka ne, ita ce Amurka.

Duk da haka, kasar ta Amurka ta yi ta yada jita-jita cewa wai “akwai barazana daga tashoshin jiragen ruwa da kasar Sin ta zuba jarin gina su a fadin duniya”, wadda ta shelanta cewa wai “tashoshin na iya samar da tallafi ga sojojin ruwan kasar Sin”. Wani abokina dan Nijeriya ya tambaye ni ra’ayina kan batun bayan da ya karanta rahoton.

  • Kasar Sin Na Goyon Bayan Shimfida Zaman Lafiya A Colombia

Lallai furucin ya ba ni dariya, mun sha jin “tarkon bashi” da “sabon salon mulkin mallaka” daga bakinsu a baya… ga shi yanzu har an alakanta tashoshin ruwa wajen shafa wa kasar Sin bakin fenti. Gaskiya sun yi iyakacin kokari wajen dakile kasar Sin.

Sinawa kan ce, ba a damuwa da rashin dalili idan ana son dora laifi kan wani, kuma wannan magana ta dace ayi amfani da ita a kan kasar Amurka, domin kuwa, Amurka ba ta taba mai da hankali a kan abubuwan da kasar Sin ta yi, a maimakon haka, kullum hankalinta na kan ta yaya za ta gano abin da zai shafa wa kasar Sin kashin kaza.

Sanin kowa ne sufurin teku ya kasance hanyar sufuri mafi muhimmanci a hada-hadar cinikin duniya, don haka ma, tashoshin jiragen ruwa na taka muhimmiyar rawa ga bunkasuwar tattalin arzikin kasa. Bisa shawarar “ziri daya da hanya daya”, kamfanonin kasar Sin sun yi ta kokarin sa hannu cikin ayyukan gina tashoshin jiragen ruwa a kasashen da suka amince da shawarar, matakin da ya yi matukar inganta samar da guraben aikin yi da ababen more rayuwa da kuma tattalin arzikin kasashen.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

Misali a Nijeriya, tashar jiragen ruwa ta Lekki da kamfanin kasar Sin ya sa hannun zuba jari da ma gina ta, ta kasance tasha mai zurfin ruwa ta zamani irinta ta farko a Nijeriya, haka kuma daya ne daga cikin jiragen ruwa mafi girma a shiyyar yammacin Afirka. Tun bayan da aka fara aiki da ita a farkon wannan shekara, tashar ta taimaka wajen fitar da kayayyakin Nijeriya zuwa ketare, musamman ma amfanin gona, an kuma yi hasashen tashar za ta samar da guraben aikin yi kimanin dubu 200 nan da shekaru masu zuwa, wadda za ta taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa tattalin arzikin kasar.

Ga shi irin wadannan tashoshin sun zamanto barazana a bakin kasar Amurka. A hakika, da yardar kasashen ne kasar Sin ke aiwatar da hadin gwiwa bisa shawarar ziri daya da hanya daya, kuma ba tare da tsoma baki cikin harkokin cikin gidansu ba, balle ma a ce ta haifar da barazana ga tsaron wata kasa. Bisa kididdigar da bankin duniya ya yi, daga shekarar 2015 zuwa ta 2030, kimanin mutane miliyan 40 ne za su fita daga kangin talauci sakamakon hadin gwiwar shawarar ziri daya da hanya daya.

Don haka ma, akasarin kasashe sun nuna yabo ga hadin gwiwar da suke yi da kasar Sin bisa shawarar ziri daya da hanya daya, akasin yadda Amurka da wasu kasashen yamma suka nuna “damuwa”. Dalilin hakan kuma shi ne hadin gwiwar ya karfafa mu’amalar tattalin arziki da al’adu a tsakanin kasashen, tare da kara karfinsu a duniya, matakin da kuma ya ba Amurka matukar damuwa, sakamakon yadda hakan ya zama barazana ga babakeren da ta kafa a duniya. Don haka, sai aka ga Amurka ta na ta kokarin yada jita jita a duniya, a kokarin bata sunan kasar Sin da ma hadin gwiwarta da kasashen duniya.

Sinawa kuma kan ce, “Sai wanda ya sa takalma ne zai san ko ya dace”. Kasashen da suke yin hadin gwiwa da kasar Sin suna da hikima da kuma kwarewa wajen tabbatar da ko hadin gwiwa ya dace ko a’a, kuma ba su bukatar “malami” ya yi musu lacca.

Duk ci gaban da za ta samu, ba za ta kafa babakere ko fadada ikonta a duniya ba, wannan alkawari ne da kasar Sin ta dauka. Amma Amurka a nata bangare, me ya sa ta kafa tarin sansanonin soja a sauran kasashen duniya?

Daga karshe, zan so in ce, duniyarmu na da girman da ya ishi kasa da kasa, ciki har da Sin da Amurka su samu ci gaba tare, ba sai an ci nasara daga faduwar wani bangare ba. Kuma ya kamata a bari kasa da kasa su zabi hanyar ci gaba da suka ga ta dace.(Mai Zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Halin Da Masu Kananan Sana’o’i Ke Ciki (2)

Next Post

Dubban Magoya Bayan Juyin Mulkin Nijar Sun Hallara A Filin Wasa Na Yamai

Related

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

2 hours ago
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

3 hours ago
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara
Daga Birnin Sin

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

4 hours ago
Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin
Daga Birnin Sin

Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

5 hours ago
Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

6 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

7 hours ago
Next Post
Dubban Magoya Bayan Juyin Mulkin Nijar Sun Hallara A Filin Wasa Na Yamai

Dubban Magoya Bayan Juyin Mulkin Nijar Sun Hallara A Filin Wasa Na Yamai

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

September 4, 2025
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

September 4, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

September 4, 2025
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

September 4, 2025
Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

September 4, 2025
Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

September 4, 2025
Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

September 4, 2025
Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

September 4, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

September 4, 2025
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

September 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.