• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
in Ra'ayi Riga
0
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Karin magana na harshen Hausa su kan kunshi ma’ana mai zurfi. Misali “Kome nisan jifa, kasa zai fado.” Ana amfani da wannan karin magana wajen kwatanta yanayin farawar wani batu, da faduwarsa, gami da yadda ya kai karshe a wani yanayi da ba wanda zai iya magancewa. Kan haka ne nake dora alkalamina game da labarin da na ji na rufe hukumar taimaka wa aikin raya kasashe ta Amurka (USAID) a kwanakin baya, wanda nan take ya tuna min da wannan karin magana.

A cewar gwamnatin Amurka, hukumar USAID ta gaza tabbatar da cewa ayyukan da ta ba da kudin tallafi sun dace da muradun Amurka, bayan da ta shafe shekaru 64 tana aiki. Ban da haka, sakataren harkokin waje na kasar Amurka, Marco Rubio, ya ce hukumar ba ta cimma wani abu ba face kafa dimbin kungiyoyin da ba na gwamnati ba (NGO) a duk fadin duniya. Kana a wuraren da ta shiga, ba a cika cimma burin raya kasa ba, yayin da yanayin rashin kwanciyar hankali kan ta’azzara, kuma kyamar Amurka na kara yaduwa.

  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
  • Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

Sai dai kafin USAID ta fado kasa tamkar wani dutsen da kasar Amurka ta jefa, ta taba samun damar “tashi sama”, ma’ana cikin dogon lokaci hukumar ta zama daya daga cikin muhimman hukumomin da Amurka ke amfani da su wajen yin tasiri kan sauran kasashe, musamman ma kasashe masu tasowa, inda hukumar ta samar da kudi da karfafa kungiyoyin NGO, da kafofin watsa labaru, da cibiyoyin bincike, da dai sauransu. Kana a cikin ayyukan da USAID ta yi, har da tallafa wa cibiyar bincike dake adawa da kasar Sin ta kasar Austiraliya (ASPI), domin ta kirkira da yada jita-jita game da Sin, da ba da tallafi ga kungiyoyin NGO da ‘yan adawa na kasashen Ukraine da Georgia don kitsa sauyin mulki a kasashen. Sa’an nan, a watan Fabrairun bana, wani dan majalisar dokokin Amurka ya ce hukumar USAID ta taba samar da kudi ga kungiyoyin ‘yan ta’adda irin su Al-Qaeda, da Boko Haram ta Najeriya.

Amma a hakika, ban da wadannan miyagun abubuwa da muka ambata, USAID ita ma ta ba da wasu gudummawa, musamman ta fuskar kiwon lafiya. Misali, wani rahoton bincike da mujallar kiwon lafiya ta Birtaniya “The Lancet” ta wallafa, ya yi hasashen cewa, raguwar kudin tallafin da aka samu sakamakon rufewar USAID, na iya haddasa mutuwar mutane fiye da miliyan 14 a duniya, ciki har da yara miliyan 4.5. Amma abin takaici shi ne, a ganin gwamnatin kasar Amurka ta yau, taimaka wa dorewar rayuwar mutane a kasashe masu tasowa “ba ta dace da muradun kasar Amurka ba”.

Hakika, da ma an san cewa tabbas Amurka za ta yi watsi da USAID. Saboda kasar ta kaddamar da shirin da zai samar da cikakken tasirinta a duniya a lokacin yakin cacar baka. Amma zuwa yanzu, tauraron kasar ya riga ya fara dishewa. Don haka ta yaya za ta samu isashen karfin cimma wani tsohon burinta da ta dade da sanyawa a rai? Idan an duba kudirin dokar “Babba kuma Kyakkyawa” (big and beautiful bill) da Amurka ta zartar kwanan nan, za a ga yadda kasar ta yi shirin rage kudin tallafin aikin jinya da na abinci, da sauran kudin tabbatar da jin dadin jama’a a cikin gidanta. Ta haka mun san cewa, ba za ta ci gaba da dora muhimmanci kan aikin jin kai a kasashen ketare ba.

Labarai Masu Nasaba

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

Ta la’akari da wannan yanayin da kasar Amurka ke ciki, ma iya cewa, ita kanta ta zama kamar wani dutse ne da ke fadowa, kuma tabbas wata rana zai taba kasa! (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

Next Post

Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

Related

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

2 days ago
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
Ra'ayi Riga

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

2 days ago
Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?
Ra'ayi Riga

Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?

7 days ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

1 week ago
Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”
Ra'ayi Riga

Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”

1 week ago
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba
Ra'ayi Riga

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

2 weeks ago
Next Post
Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

LABARAI MASU NASABA

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

July 25, 2025
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.