ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

by Sadiq
1 year ago
Yobe

Gwamnatin Jihar Yobe ta sanar da rufe wasu kasuwanni uku na mako-mako na ɗan wani lokaci, saboda tsoron yiwuwar hare-haren Boko Haram.

Kasuwannin da abin ya shafa su ne na Katarko, Kukareta da Buni Yadi, dukkaninsu a Ƙaramar Hukumar Gujba.

  • Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota
  • ’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3

An rufe su ne domin taimakawa aikin da jami’an tsaro ke yi wajen yaƙar ’yan ta’adda a faɗin jihar.

ADVERTISEMENT

A cewar Mai Bai Wai Gwamnan Yobe Shawara Kan Sha’anin Tsaro, Birgediya Janar Dahiru Abdulsalam (mai ritaya), an rufe kasuwannin ne don bai wa jami’an tsaro damar gudanar da ayyukansu cikin sauƙi tare da inganta tsaro a yankunan da abin ya shafa.

Ya ce, “Wannan mataki na ɗan lokaci ne da zai taimaka wajen cimma wasu muhimman manufofi na tsaro a jihar.”

LABARAI MASU NASABA

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Birgediya Janar Abdulsalam ya roƙi jama’a da su bai wa jami’an tsaro haɗin kai, duk da cewa rufe kasuwannin na iya kawo wata matsala ga rayuwar yau da kullum.

“Gwamnati na ƙoƙarin ganin an rage tasirin da rufe kasuwannin ka iya haifarwa ga al’umma. Muna roƙon ku fahimce mu saboda zaman lafiya da tsaro,” in ji shi.

Ya kuma tabbatar wa mazauna yankunan cewa za a sake buɗe kasuwannin nan ba da jimawa ba, idan aka kammala aikin tsaro da ake gudanarwa.

Kasuwannin da aka rufe suna daga cikin manyan kasuwanni a wannan yanki na Jihar Yobe.

Wani mazaunin Kukareta ya shaida wa wakilinmu cewa ba su san dalilin rufe kasuwannin ba, kawai ji suka yi an ce an bayar da umarni daga sama.

Wani ɗan kasuwa daga Buni Yadi da ya nemi a sakaya sunansa ya ce ya ji an ce an rufe kasuwannin ne saboda wasu ’yan kasuwa na sayar wa Boko Haram kayan abinci.

Ya ce, “Ban san da yawa ba, amma abin da na ji shi ne an bayar da umarni a ranar Litinin, suna cewa masu sayar da abinci a waɗannan kasuwanni suna taimakawa Boko Haram wajen siyan kayan abinci.”

MASU ALAKA

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato
Manyan Labarai

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027
Manyan Labarai

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara
Manyan Labarai

An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

July 12, 2026
Next Post
Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

LABARAI MASU NASABA

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

July 12, 2026
Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

July 12, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

July 12, 2026
Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.