ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Amurka

Karin magana na harshen Hausa su kan kunshi ma’ana mai zurfi. Misali “Kome nisan jifa, kasa zai fado.” Ana amfani da wannan karin magana wajen kwatanta yanayin farawar wani batu, da faduwarsa, gami da yadda ya kai karshe a wani yanayi da ba wanda zai iya magancewa. Kan haka ne nake dora alkalamina game da labarin da na ji na rufe hukumar taimaka wa aikin raya kasashe ta Amurka (USAID) a kwanakin baya, wanda nan take ya tuna min da wannan karin magana.

A cewar gwamnatin Amurka, hukumar USAID ta gaza tabbatar da cewa ayyukan da ta ba da kudin tallafi sun dace da muradun Amurka, bayan da ta shafe shekaru 64 tana aiki. Ban da haka, sakataren harkokin waje na kasar Amurka, Marco Rubio, ya ce hukumar ba ta cimma wani abu ba face kafa dimbin kungiyoyin da ba na gwamnati ba (NGO) a duk fadin duniya. Kana a wuraren da ta shiga, ba a cika cimma burin raya kasa ba, yayin da yanayin rashin kwanciyar hankali kan ta’azzara, kuma kyamar Amurka na kara yaduwa.

  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
  • Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

Sai dai kafin USAID ta fado kasa tamkar wani dutsen da kasar Amurka ta jefa, ta taba samun damar “tashi sama”, ma’ana cikin dogon lokaci hukumar ta zama daya daga cikin muhimman hukumomin da Amurka ke amfani da su wajen yin tasiri kan sauran kasashe, musamman ma kasashe masu tasowa, inda hukumar ta samar da kudi da karfafa kungiyoyin NGO, da kafofin watsa labaru, da cibiyoyin bincike, da dai sauransu. Kana a cikin ayyukan da USAID ta yi, har da tallafa wa cibiyar bincike dake adawa da kasar Sin ta kasar Austiraliya (ASPI), domin ta kirkira da yada jita-jita game da Sin, da ba da tallafi ga kungiyoyin NGO da ‘yan adawa na kasashen Ukraine da Georgia don kitsa sauyin mulki a kasashen. Sa’an nan, a watan Fabrairun bana, wani dan majalisar dokokin Amurka ya ce hukumar USAID ta taba samar da kudi ga kungiyoyin ‘yan ta’adda irin su Al-Qaeda, da Boko Haram ta Najeriya.

ADVERTISEMENT

Amma a hakika, ban da wadannan miyagun abubuwa da muka ambata, USAID ita ma ta ba da wasu gudummawa, musamman ta fuskar kiwon lafiya. Misali, wani rahoton bincike da mujallar kiwon lafiya ta Birtaniya “The Lancet” ta wallafa, ya yi hasashen cewa, raguwar kudin tallafin da aka samu sakamakon rufewar USAID, na iya haddasa mutuwar mutane fiye da miliyan 14 a duniya, ciki har da yara miliyan 4.5. Amma abin takaici shi ne, a ganin gwamnatin kasar Amurka ta yau, taimaka wa dorewar rayuwar mutane a kasashe masu tasowa “ba ta dace da muradun kasar Amurka ba”.

Hakika, da ma an san cewa tabbas Amurka za ta yi watsi da USAID. Saboda kasar ta kaddamar da shirin da zai samar da cikakken tasirinta a duniya a lokacin yakin cacar baka. Amma zuwa yanzu, tauraron kasar ya riga ya fara dishewa. Don haka ta yaya za ta samu isashen karfin cimma wani tsohon burinta da ta dade da sanyawa a rai? Idan an duba kudirin dokar “Babba kuma Kyakkyawa” (big and beautiful bill) da Amurka ta zartar kwanan nan, za a ga yadda kasar ta yi shirin rage kudin tallafin aikin jinya da na abinci, da sauran kudin tabbatar da jin dadin jama’a a cikin gidanta. Ta haka mun san cewa, ba za ta ci gaba da dora muhimmanci kan aikin jin kai a kasashen ketare ba.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Ta la’akari da wannan yanayin da kasar Amurka ke ciki, ma iya cewa, ita kanta ta zama kamar wani dutse ne da ke fadowa, kuma tabbas wata rana zai taba kasa! (Bello Wang)

Amurka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Amurka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.