• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ECOWAS Ta Bada Umarnin Daukar Matakin Soji A Kan Gwamnatin Nijar

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai, Da ɗumi-ɗuminsa
0
ECOWAS Ta Bada Umarnin Daukar Matakin Soji A Kan Gwamnatin Nijar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS), ta umarci rundunar ta da ta dauki mataki da nufin mayar da tsarin mulkin Jamhuriyar Nijar.

ECOWAS, ta bayyana hakan ne a lokacin da ta gabatar da kudurinta dangane da juyin mulkin da aka yi a Nijar a wani taro na musamman da aka gudanar a Abuja ranar Alhamis.

  • Golan Real Madrid Courtois Zai Yi Jinyar Watanni Bayan Samun Rauni
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Soke “Doka Game Da Taiwan”

Baya ga kiran daukar mataki, ECOWAS ta kuma yi kira ga kungiyar tarayyar Afrika (AU), da kasashen da ta ke hulda da kuma cibiyoyin da abin ya shafa da su goyi bayan kudurin da kungiyar ta dauka.

ECOWAS ta bayyana rashin jin dadinta ganin yadda duk wani yunkurin tattaunawa da gwamnatin mulkin soji a Nijar ya ci tura.

Bugu da kari, ECOWAS ta yi kakkausar suka ga ci gaba da tsare shugaba Mohamed Bazoum da ‘yan uwansa.

Labarai Masu Nasaba

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

“Hukumar ta yi la’akari da takardar da shugaban ECOWAS ya gabatar kan halin da ake ciki a Jamhuriyar Nijar, da kuma yadda ECOWAS ta shiga tsakani tun bayan babban taronta na karshe;

“kuma mun yin la’akari da rahotannin wakilan Nijar da sauran wurare daban-daban;

“Mun yi la’akari da rahoto da shawarwarin kwamitin hafsoshin tsaro na ECOWAS;

“Mun tattauna kan sabon ci gaban da aka samu a Nijar tun bayan babban taron koli na karshe da aka gudanar a ranar 30 ga Yuli, 2023.

“An yi la’akari da cewa, duk kokarin diflomasiyya da ECOWAS ta yi, wajen magance rikicin, shugabannin sojin Jamhuriyar Nijar sun yi watsi da su.

“Sakamakon cikar wa’adin mako guda da aka bayar na mayar da tsarin mulki a Jamhuriyar Nijar mun yake wannan shawara.

“ECOWAS ta nanata kakkausar suka ga juyin mulki da kuma ci gaba da tsare Shugaba Mohammed Bazoam da iyalansa da kuma mambobin gwamnatinsa ba bisa ka’ida ba.

“Kaddamar da kudurin hukumar ECOWAS na warware rikicin.

“Tabbatar da duk matakai musamman na rufe kan iyakoki da tsauraran dokar hana tafiye-tafiye a kan duk mutane ko kungiyoyin mutanen da ayyukansu ke kawo cikas ga duk kokarin da ake na zaman lafiya da nufin tabbatar da ingantaccen tsarin mayar da tsarin mulki.

“Mun gargadi kasashe ta hanyar kawo cikas wajen warware rikicin Nijar cikin lumana game da illar matakin da suka dauka a gaban al’umma.

“Kira ga kungiyar Tarayyar Afirka da ta amince da duk shawarar da hukumar ECOWAS ta dauka kan halin da ake ciki a Nijar.

“Dukkanin kasashe da cibiyoyin hadin gwiwa ciki har da Majalisar Dinkin Duniya da su tallafa wa kungiyar ECOWAS, a kokarinta na tabbatar da mayar da tsarin mulkin kasar cikin gaggawa.”

ECOWAS ta jadadda aniyarta na tabbatar da mulkin dimokuradyya a Jamhuriyar Nijar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BazoumECOWASJuyin MulkiNijarSojojiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Golan Real Madrid Courtois Zai Yi Jinyar Watanni Bayan Samun Rauni

Next Post

NSCDC Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 10, Ta Kafa ‘Yan Sintiri

Related

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

2 hours ago
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

12 hours ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

21 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

1 day ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

2 days ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

2 days ago
Next Post
NSCDC Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 10, Ta Kafa ‘Yan Sintiri

NSCDC Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 10, Ta Kafa 'Yan Sintiri

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.