Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) ta kama tsohon kakakin majalisar dokokin jihar Filato, Mista Moses Thomas Sule da wasu tsaffin ‘yan majalisa 14 bisa zargin karkatar da kudade.
An kama tsoffin ‘yan majalisar ne biyo bayan korafi da wasu ‘yan jihar suka yi a kansu bisa zarginsu da karya dokar ka’idojin aiki ta 2022, da kuma cin zarafin tsarin saye da sayarwa.
- Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo
- An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna
Wasu daga cikin tsoffin ‘yan majalisar 14 da aka kama sun hada da: Gwottson Fom, Sani Abubakar, Jwe Philip Gwom, Thomas Dantong, Happiness Mathew Akawu, Cornelius Dotyok, da Agbalak Ibrahim.
Sauran sun hada da: Danjuma Azi, Fwangje Bala Ndat, Salome Tanimu Wanglet, Namba Rimuyat, Nimchak Rims, Ishaku Maren da Paul Datugun.
Kakakin hukumar ta EFCC, Dele Oyewale, wanda ya tabbatar da kamun, ya ce bincike ya nuna cewa tsaffin ‘yan majalisar sun shafe watanni shida ne kawai a kan karagar mulki, sannan gwamnatin jihar ta siya musu motocin alfarma.
Bincike ya kuma nuna cewa, motocin da aka ce kudinsu ya kai Naira biliyan 2.5. Bayan sun sauka akan mukaminsu, sun tafi da motocin kuma duk kokarin da aka yi na su dawo da su, lamarin ya ci tura.
Sai da gwamnatin jihar ta sake sayo wa ‘yan majalisar na yanzu motocin da kudinsu ya kai kimanin naira biliyan biyu.
Oyewale ya tabbatar da cewa nan ba da jimawa ba za a gurfanar da tsohon shugaban majalisar da sauran mambobin a kotu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp