ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

by Sulaiman
1 year ago
Zamfara

Tsohon Shugaban Nijeriya, Cif Olusegun Obasanjo ya yaba wa Gwamna Dauda Lawal bisa manyan nasarorin da ya samu, inda ya jaddada kyakkyawan tasirin shugabancinsa a Jihar Zamfara.

 

A ranar Talata ne tsohon shugaban ƙasar ya ƙaddamar da asibitin ƙwararru na Yariman Bakura da wasu manyan tituna guda biyu a Gusau, babban birnin jihar Zamfara.

ADVERTISEMENT
  • Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
  • Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa a karon farko jihar ta samu na’urar ɗaukar hoton jikin ɗan adam mai gani jar hanyi, ta ‘CT Scan,’ da wata na’urar ita mai ɗaukan hoton dukkan sannan mutum, ta ‘MRI Machine’ a asibitin ƙwararru na Yariman Bakura da aka gyara.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

A yayin ƙaddamar da asibitin ƙwararrun, tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ya buƙaci gwamna Lawal da ya ci gaba da gudanar da ayyukan ceto har sai Zamfara ta kasance ɗaya daga cikin manyan jihohin Nijeriya.

 

Tsohon shugaban ƙasar ya ce: “A yau ina jihar Zamfara ne domin na ga ingantacciya, wadda ta ci gaba, mai ci gaba kuma sabuwar Zamfara a ƙarƙashin jagorancin ka.

 

“Ga mu nan. Abubuwa biyu sun ba ni mamaki: Kwamishinan lafiya ya bayyana cewa kun samar da na’urorin CT scan da MRI Machine, na san wasu asibitocin koyarwa ba su da CT scan da MRI, wasu kuma suna da shi amma ba sa aiki. Ku ga na ku, yana aiki ga al’umma.

 

“Na yi matuƙar farin cikin kasancewa a nan, don ƙaddamar da wannan asibitin da aka gyara da kuma saka kayan aiki na zamani don jin daɗin duk wanda zai zo nan.”

 

Da yake ƙaddamar da titin Zannah zuwa Abarma, tsohon shugaban ƙasa Obasanjo ya bayyana cewa, Gwamna Lawal na mayar da Zamfara jiha ta zamani.

 

“A bisa abubuwan da na gani da idanu na da kuma wanda na ji, mu abokan haɗin gwiwa ne a ci gaba. Ina roƙon ka da ka ci gaba da inganta jihar Zamfara a tsawon shekaru takwas da gwamnatin ka za ta yi.”

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya gode wa tsohon shugaban ƙasa Obasanjo bisa amsa gayyatar da aka yi masa na ƙaddamar da muhimman ayyuka a jihar.

 

“Ranka ya daɗe, a madadin ɗaukacin al’ummar jihar Zamfara, muna godiya da karrama mu ga amsa gayyatar da muka yi maka, da kuma maraba da zuwa gidanka na biyu, Jihar Zamfara, Jihar da ka ke kyauna a zuciyarka, domin sana’armu ta farko a nan ita ce noma, kuma wani abu ne da ka ke sha’awa.

 

“Asibitin ƙwararru na Ahmad Sani Yariman Bakura ya bi tsarin faɗaɗawa da ingantawa, an kuma gina sabbin gine-gine, a yanzu haka likitocin suna da sabbin gidajen zama da aka kammala, waɗanda suka haɗa da rukunin gida mai ɗakuna biyu da mai uku, da kuma wurin zama da ya dace da Babban Daraktan Lafiya.

 

“An kuma samar da filin da mara lafiya zai shaƙatawa cikin natsuwa tare da ƙawata yanayin asibitin. Mun kuma inganta hanyoyin cikin asibitin don sauƙaƙa zirga-zirga da ƙayatar da harabar asibitin.

 

“Sabbin cibiyoyin da aka gina su ne Sashin Kula da Mata (O&G), sabon rukunin Radiology, sashin ɗakin gwaje-gwaje, da filin shaƙatawa na marasa lafiya.

 

“Ginshiƙi shi ne gyara muhimman sassa guda 14, waɗanda dukkansu an sake farfaɗo da su tare da inganta su zuwa matsayin zamani.

 

“Mun saka duk waɗannan kayayyaki na zamani a wuraren da suka dace kuma masu muhimmanci. Waɗannan sun haɗa da saka na’urori na zamani a bangaren don radiology, wankin ƙoda, tiyata, ophthalmology, ENT, physiotherapy, endoscopy, echocardiography, haƙori, da kuma kula da lafiya gaba ɗaya.

 

“An kuma ba wa asibitin sabbin gadaje na majiyyata, na’urorin lantarki, kayan ɗaki, da kayayyakin tattara shara don tabbatar da tsaftar muhalli da bin ƙa’idojin tsabta na duniya.”

 

Gwamnan ya jaddada cewa asibitin yana da ingantattun kayan aiki don aiki a matsayin cibiyar tuntuɓar likitoci, ingantaccen wurin horar da ma’aikatan kiwon lafiya kuma cibiyar bincike da ƙididdiga ta likitanci.

 

Sauran ayyukan da aka ƙaddamar sun haɗa da titin Zannah zuwa Abarma da titin Tsalha Bungudu zuwa Kwanar Birnin Ruwa, duk a Gusau babban birnin jihar.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan

Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.