ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

by Sulaiman
1 year ago
Zamfara

Tsohon Shugaban Nijeriya, Cif Olusegun Obasanjo ya yaba wa Gwamna Dauda Lawal bisa manyan nasarorin da ya samu, inda ya jaddada kyakkyawan tasirin shugabancinsa a Jihar Zamfara.

 

A ranar Talata ne tsohon shugaban ƙasar ya ƙaddamar da asibitin ƙwararru na Yariman Bakura da wasu manyan tituna guda biyu a Gusau, babban birnin jihar Zamfara.

ADVERTISEMENT
  • Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
  • Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa a karon farko jihar ta samu na’urar ɗaukar hoton jikin ɗan adam mai gani jar hanyi, ta ‘CT Scan,’ da wata na’urar ita mai ɗaukan hoton dukkan sannan mutum, ta ‘MRI Machine’ a asibitin ƙwararru na Yariman Bakura da aka gyara.

 

LABARAI MASU NASABA

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

A yayin ƙaddamar da asibitin ƙwararrun, tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ya buƙaci gwamna Lawal da ya ci gaba da gudanar da ayyukan ceto har sai Zamfara ta kasance ɗaya daga cikin manyan jihohin Nijeriya.

 

Tsohon shugaban ƙasar ya ce: “A yau ina jihar Zamfara ne domin na ga ingantacciya, wadda ta ci gaba, mai ci gaba kuma sabuwar Zamfara a ƙarƙashin jagorancin ka.

 

“Ga mu nan. Abubuwa biyu sun ba ni mamaki: Kwamishinan lafiya ya bayyana cewa kun samar da na’urorin CT scan da MRI Machine, na san wasu asibitocin koyarwa ba su da CT scan da MRI, wasu kuma suna da shi amma ba sa aiki. Ku ga na ku, yana aiki ga al’umma.

 

“Na yi matuƙar farin cikin kasancewa a nan, don ƙaddamar da wannan asibitin da aka gyara da kuma saka kayan aiki na zamani don jin daɗin duk wanda zai zo nan.”

 

Da yake ƙaddamar da titin Zannah zuwa Abarma, tsohon shugaban ƙasa Obasanjo ya bayyana cewa, Gwamna Lawal na mayar da Zamfara jiha ta zamani.

 

“A bisa abubuwan da na gani da idanu na da kuma wanda na ji, mu abokan haɗin gwiwa ne a ci gaba. Ina roƙon ka da ka ci gaba da inganta jihar Zamfara a tsawon shekaru takwas da gwamnatin ka za ta yi.”

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya gode wa tsohon shugaban ƙasa Obasanjo bisa amsa gayyatar da aka yi masa na ƙaddamar da muhimman ayyuka a jihar.

 

“Ranka ya daɗe, a madadin ɗaukacin al’ummar jihar Zamfara, muna godiya da karrama mu ga amsa gayyatar da muka yi maka, da kuma maraba da zuwa gidanka na biyu, Jihar Zamfara, Jihar da ka ke kyauna a zuciyarka, domin sana’armu ta farko a nan ita ce noma, kuma wani abu ne da ka ke sha’awa.

 

“Asibitin ƙwararru na Ahmad Sani Yariman Bakura ya bi tsarin faɗaɗawa da ingantawa, an kuma gina sabbin gine-gine, a yanzu haka likitocin suna da sabbin gidajen zama da aka kammala, waɗanda suka haɗa da rukunin gida mai ɗakuna biyu da mai uku, da kuma wurin zama da ya dace da Babban Daraktan Lafiya.

 

“An kuma samar da filin da mara lafiya zai shaƙatawa cikin natsuwa tare da ƙawata yanayin asibitin. Mun kuma inganta hanyoyin cikin asibitin don sauƙaƙa zirga-zirga da ƙayatar da harabar asibitin.

 

“Sabbin cibiyoyin da aka gina su ne Sashin Kula da Mata (O&G), sabon rukunin Radiology, sashin ɗakin gwaje-gwaje, da filin shaƙatawa na marasa lafiya.

 

“Ginshiƙi shi ne gyara muhimman sassa guda 14, waɗanda dukkansu an sake farfaɗo da su tare da inganta su zuwa matsayin zamani.

 

“Mun saka duk waɗannan kayayyaki na zamani a wuraren da suka dace kuma masu muhimmanci. Waɗannan sun haɗa da saka na’urori na zamani a bangaren don radiology, wankin ƙoda, tiyata, ophthalmology, ENT, physiotherapy, endoscopy, echocardiography, haƙori, da kuma kula da lafiya gaba ɗaya.

 

“An kuma ba wa asibitin sabbin gadaje na majiyyata, na’urorin lantarki, kayan ɗaki, da kayayyakin tattara shara don tabbatar da tsaftar muhalli da bin ƙa’idojin tsabta na duniya.”

 

Gwamnan ya jaddada cewa asibitin yana da ingantattun kayan aiki don aiki a matsayin cibiyar tuntuɓar likitoci, ingantaccen wurin horar da ma’aikatan kiwon lafiya kuma cibiyar bincike da ƙididdiga ta likitanci.

 

Sauran ayyukan da aka ƙaddamar sun haɗa da titin Zannah zuwa Abarma da titin Tsalha Bungudu zuwa Kwanar Birnin Ruwa, duk a Gusau babban birnin jihar.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • Sulaiman
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

MASU ALAKA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Manyan Labarai

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft
Labarai

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Zamfara
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Next Post
Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan

Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Zamfara

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Zamfara

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.