ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

by Sulaiman
1 year ago
Zamfara

Tsohon Shugaban Nijeriya, Cif Olusegun Obasanjo ya yaba wa Gwamna Dauda Lawal bisa manyan nasarorin da ya samu, inda ya jaddada kyakkyawan tasirin shugabancinsa a Jihar Zamfara.

 

A ranar Talata ne tsohon shugaban ƙasar ya ƙaddamar da asibitin ƙwararru na Yariman Bakura da wasu manyan tituna guda biyu a Gusau, babban birnin jihar Zamfara.

ADVERTISEMENT
  • Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
  • Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa a karon farko jihar ta samu na’urar ɗaukar hoton jikin ɗan adam mai gani jar hanyi, ta ‘CT Scan,’ da wata na’urar ita mai ɗaukan hoton dukkan sannan mutum, ta ‘MRI Machine’ a asibitin ƙwararru na Yariman Bakura da aka gyara.

 

LABARAI MASU NASABA

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

A yayin ƙaddamar da asibitin ƙwararrun, tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ya buƙaci gwamna Lawal da ya ci gaba da gudanar da ayyukan ceto har sai Zamfara ta kasance ɗaya daga cikin manyan jihohin Nijeriya.

 

Tsohon shugaban ƙasar ya ce: “A yau ina jihar Zamfara ne domin na ga ingantacciya, wadda ta ci gaba, mai ci gaba kuma sabuwar Zamfara a ƙarƙashin jagorancin ka.

 

“Ga mu nan. Abubuwa biyu sun ba ni mamaki: Kwamishinan lafiya ya bayyana cewa kun samar da na’urorin CT scan da MRI Machine, na san wasu asibitocin koyarwa ba su da CT scan da MRI, wasu kuma suna da shi amma ba sa aiki. Ku ga na ku, yana aiki ga al’umma.

 

“Na yi matuƙar farin cikin kasancewa a nan, don ƙaddamar da wannan asibitin da aka gyara da kuma saka kayan aiki na zamani don jin daɗin duk wanda zai zo nan.”

 

Da yake ƙaddamar da titin Zannah zuwa Abarma, tsohon shugaban ƙasa Obasanjo ya bayyana cewa, Gwamna Lawal na mayar da Zamfara jiha ta zamani.

 

“A bisa abubuwan da na gani da idanu na da kuma wanda na ji, mu abokan haɗin gwiwa ne a ci gaba. Ina roƙon ka da ka ci gaba da inganta jihar Zamfara a tsawon shekaru takwas da gwamnatin ka za ta yi.”

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya gode wa tsohon shugaban ƙasa Obasanjo bisa amsa gayyatar da aka yi masa na ƙaddamar da muhimman ayyuka a jihar.

 

“Ranka ya daɗe, a madadin ɗaukacin al’ummar jihar Zamfara, muna godiya da karrama mu ga amsa gayyatar da muka yi maka, da kuma maraba da zuwa gidanka na biyu, Jihar Zamfara, Jihar da ka ke kyauna a zuciyarka, domin sana’armu ta farko a nan ita ce noma, kuma wani abu ne da ka ke sha’awa.

 

“Asibitin ƙwararru na Ahmad Sani Yariman Bakura ya bi tsarin faɗaɗawa da ingantawa, an kuma gina sabbin gine-gine, a yanzu haka likitocin suna da sabbin gidajen zama da aka kammala, waɗanda suka haɗa da rukunin gida mai ɗakuna biyu da mai uku, da kuma wurin zama da ya dace da Babban Daraktan Lafiya.

 

“An kuma samar da filin da mara lafiya zai shaƙatawa cikin natsuwa tare da ƙawata yanayin asibitin. Mun kuma inganta hanyoyin cikin asibitin don sauƙaƙa zirga-zirga da ƙayatar da harabar asibitin.

 

“Sabbin cibiyoyin da aka gina su ne Sashin Kula da Mata (O&G), sabon rukunin Radiology, sashin ɗakin gwaje-gwaje, da filin shaƙatawa na marasa lafiya.

 

“Ginshiƙi shi ne gyara muhimman sassa guda 14, waɗanda dukkansu an sake farfaɗo da su tare da inganta su zuwa matsayin zamani.

 

“Mun saka duk waɗannan kayayyaki na zamani a wuraren da suka dace kuma masu muhimmanci. Waɗannan sun haɗa da saka na’urori na zamani a bangaren don radiology, wankin ƙoda, tiyata, ophthalmology, ENT, physiotherapy, endoscopy, echocardiography, haƙori, da kuma kula da lafiya gaba ɗaya.

 

“An kuma ba wa asibitin sabbin gadaje na majiyyata, na’urorin lantarki, kayan ɗaki, da kayayyakin tattara shara don tabbatar da tsaftar muhalli da bin ƙa’idojin tsabta na duniya.”

 

Gwamnan ya jaddada cewa asibitin yana da ingantattun kayan aiki don aiki a matsayin cibiyar tuntuɓar likitoci, ingantaccen wurin horar da ma’aikatan kiwon lafiya kuma cibiyar bincike da ƙididdiga ta likitanci.

 

Sauran ayyukan da aka ƙaddamar sun haɗa da titin Zannah zuwa Abarma da titin Tsalha Bungudu zuwa Kwanar Birnin Ruwa, duk a Gusau babban birnin jihar.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa
  • Sulaiman
    Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass
  • Sulaiman
    Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

MASU ALAKA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

June 27, 2026
Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji
Manyan Labarai

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

June 27, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Labarai

Bidiyo: Turji Ya Yi Iƙirarin Ɗaukar Alhakin Kashe Wasu Sojoji

June 27, 2026
Next Post
Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan

Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

June 27, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

June 27, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

June 27, 2026
Zamfara

Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma

June 27, 2026
Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

June 27, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Bidiyo: Turji Ya Yi Iƙirarin Ɗaukar Alhakin Kashe Wasu Sojoji

June 27, 2026
Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A  Titin Bypass

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

June 26, 2026
Disu

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.