• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

El-Rufai Ya Hakura Da Tayin Minista, Ya Zabi Sani Don ya Maye Gurbinsa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
El-Rufai Ya Hakura Da Tayin Minista, Ya Zabi Sani Don ya Maye Gurbinsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon  gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, ya hakura gami da cire ransa daga sha’awar zama minista a karkakashin mulkin shugaba Tinubu kamar yadda jaridar Premium Times ta nakalto.

Wata majiya daga fadar shugaban kasa ta ce, Nasir El-Rufai ya shaida wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu yayin wata ganawa da suka yi a ranar Talata cewa, shi kam yanzu bai da ra’ayin zama minista, amma duk da hakan zai bada tasa gudunmawar wajen cigaban Nijeriya a matsayinsa na dan kasa.

  • Mun Dauki Darasi A Zaben 2023 – Shugaban INEC
  • Sin Ta Kara Ware Yuan Biliyan 1.46 Don Taimakawa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

“Ya shaida wa shugaban kasa cewa ya na son ya maida hankalinsa kan darasin dakta a jami’ar The Netherlands,” a cewar daya daga cikin majiyoyin.

Wata majiyar kuma ta shaida cewar tsohon gwamnan ya bada shawarar a zabi Jafaru Ibrahim Sani daga jihar Kaduna a matsayin minista da zai maye gurbin ta’ayin da aka masa da farko, a cewarsa, shugaban kasa zai samesa a matsayin mutum mai matukar amfani.

Shi dai Sani ya yi aiki a matsayin kwamishina a ma’aikatu har uku a karkashin mulkin gwamna Nasiru El-Rufai.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

Nasiru dai ya gana da shugaban kasa a fadar shugaban kasa da ke Abuja bayan da majalisar dattawa ta tantance da amincewa da zabin ministoci 45 cikin 48 da shugaban kasa ya aike musu.

Kodayake, majalisar ta ki amince da zabin Nasir El-Rufai da wasu mutum biyu bisa rahoton tsaro da bai amince da su ba.

Sauran mutum biyun da majalisar ta ki amince da nadinsu su ne tsohon sanata daga Taraba, Sani Danladi, da kuma Stella Okotete daga jihar Delta.

Majiyoyin sun ce a lokacin da El-Rufai ya ji matakin da Majalisa ta tsayar kansa yana ma can kasar Landan nan da nan ya dawo Nijeriya a ranar Litinin domin neman ganawa da shugaban kasa kan batun.

A cewar majaliyar a yayin zaman shugaban kasa da El-Rufai, Tinubu ya fada masa cewar ya amshi wasu korafe-korafe a kan nadin da ya amsa na minista.

Sai dai shugaban ya nemi awanni 24 domin ya sake bibiyar korafe-korafen da rahoton tsaro na SSS domin ganin an samu damar da majalisa za ta iya amincewa da shi.

A lokacin ne sai El-Rufai ya amsa da cewa shi yanzu ba ya da ra’ayin zama minista kuma, tun da wasu da suke makale a jikin shugaban kasan ba su da ra’ayin zamansa minista.

Lokacin da aka tuntubi kakakin Malam Nasir, Muyiwa Adekeye, ya ki cewa uffan kan labarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Dauki Darasi A Zaben 2023 – Shugaban INEC

Next Post

Matakin Amurka Na Neman Takaita Zuba Jari A Kasar Sin Illata Kai Ne

Related

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

2 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

4 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

5 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

6 hours ago
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
Labarai

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

8 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

9 hours ago
Next Post
Matakin Amurka Na Neman Takaita Zuba Jari A Kasar Sin Illata Kai Ne

Matakin Amurka Na Neman Takaita Zuba Jari A Kasar Sin Illata Kai Ne

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.