ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dauki Darasi A Zaben 2023 – Shugaban INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
INEC

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Mahmood Yakubu ya bayyana cewa sun yi matukar daukar darasi a zaben 2023, sannan za su kara kwazo a zaben gwamnoni da zai gudanar a jihohin Kogi, Imo da kuma Bayelsa.

Ya kara da cewa hukumar ta gamsu da irin martanin da ta samu a yayin bitar bayan zaben 2023 da hukumar ta shirya.

  • NSCDC Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 10, Ta Kafa ‘Yan Sintiri
  • Yadda Amurka Ke Kwaton Albarkatun Kasa Da Kasa Da Sunan Yaki Da Ta’addanci

Shugaban INEC ya bayyana hakan ne a jim kadan bayan kammala bitar zaben 2023 na kwanaki uku da ya gudana a Jihar Legas, inda ya tabbatar da cewa za a magance matsalolin da suka faru a lokacin zaben da tare da yin amfani da shawarwarin da hukumar ta samu domin inganta zaben kasar nan, wanda hukumar za ta fara yin gwaji a zabukan gwamnoni da za su gudana a jihohin Kogi, Imo da kuma Bayelsa.

ADVERTISEMENT

“Mun yi wa ‘yan Nijeriya alkawarin cewa za mu gudanar da bitar zaben 2023 a cikin wata daya. Mun fara ne tun daga ranar 4 ga watan Yulin har zuwa 4 ga watan Agusta, mun samu korafe-korafe mai matukar yawan gaske. Mun fara gudanar da taron tattaunawa na shawarwari da kwamishinoninmu da ke jihohi, sannan muka zarce har zuwa wurin kungiyoyin sufuri, kafin muka shigo da jam’iyyu da sauran kungiyoyin fararen huda da dai sauransu. Gaba daya dai, muna samun kwarin gwiwa ta hanyar martanin masu ruwa da tsaki a fadin hukumar da irin gudunmawar da suka bayarwa.

“Mun samu matsaloli masu yawa tu daga wurin tantance masu kada kuri’a har zuwa saka sakamakon zabe a na’ura, sai dai mun samu shawarwari a kan haka.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

“Akwai batun kalubalen kai kayayyakin zabe da yadda za a fara zabuka a kan lokaci da da samar da katin zabe da kuma amsa katin da sauransu. Muna samu korafe-korafe masu yawa kuma mun samu shawarwari a kan lamarin, inda wadanda hukumar za ta iya magancesu a ofis, za ta yi hakan, wadanda kuma ke bukatar gyara ga dokokin zabe ne ko kundin tsarin mulki za mu kai su zauren majalisar kasa domin duba lamarin. Don haka mun yi farin ciki da martanin da muka samu da kuma tattaunawa da muka yi a hukumar. Abu mafi muhimmanci ga hukumar shi ne, mun ji ta bakin ‘yan Nijeriya kuma hakan zai ba mu damar komawa kan turbar hukumar domin ci gaba da inganta zaben kasar nan.

“Bayan mun samu wadannan korafe-korafe, hakan zai ba mu damar yin gyare-gyare a zabukan gwamnoni da za su gudana a jihohin Bayelsa, Imo da kuma Kogi a watan Nuwamba, domin za mu kaddamar da wasu daga cikin shawarwarin da muka samu wadanda suka kunshi hukumar, amma wadanda suka kunshi majalisa, majalisar kasa za ta yi aiki ne bisa tanadin dokokin kasar nan.

“Haka kuma akwai wata damar da muka da ita, saboda a halin yanzu kwai zaben cike gurbi har guda hudu da suka hada da mazaba Surulere 1 a Jihar Legas da mazabar Jalingo da ke Jihar Taraba da mazabar Chibok da ke Jihar Borno State da kuma mazabar Chikun da ke Jihar Kaduna. Za mu ci gaba da kaddamar da wasu shawarwarin a zabukan cike gurbi da ke tafe.”

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
El-Rufai Ya Hakura Da Tayin Minista, Ya Zabi Sani Don ya Maye Gurbinsa

El-Rufai Ya Hakura Da Tayin Minista, Ya Zabi Sani Don ya Maye Gurbinsa

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.