ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dauki Darasi A Zaben 2023 – Shugaban INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
INEC

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Mahmood Yakubu ya bayyana cewa sun yi matukar daukar darasi a zaben 2023, sannan za su kara kwazo a zaben gwamnoni da zai gudanar a jihohin Kogi, Imo da kuma Bayelsa.

Ya kara da cewa hukumar ta gamsu da irin martanin da ta samu a yayin bitar bayan zaben 2023 da hukumar ta shirya.

  • NSCDC Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 10, Ta Kafa ‘Yan Sintiri
  • Yadda Amurka Ke Kwaton Albarkatun Kasa Da Kasa Da Sunan Yaki Da Ta’addanci

Shugaban INEC ya bayyana hakan ne a jim kadan bayan kammala bitar zaben 2023 na kwanaki uku da ya gudana a Jihar Legas, inda ya tabbatar da cewa za a magance matsalolin da suka faru a lokacin zaben da tare da yin amfani da shawarwarin da hukumar ta samu domin inganta zaben kasar nan, wanda hukumar za ta fara yin gwaji a zabukan gwamnoni da za su gudana a jihohin Kogi, Imo da kuma Bayelsa.

ADVERTISEMENT

“Mun yi wa ‘yan Nijeriya alkawarin cewa za mu gudanar da bitar zaben 2023 a cikin wata daya. Mun fara ne tun daga ranar 4 ga watan Yulin har zuwa 4 ga watan Agusta, mun samu korafe-korafe mai matukar yawan gaske. Mun fara gudanar da taron tattaunawa na shawarwari da kwamishinoninmu da ke jihohi, sannan muka zarce har zuwa wurin kungiyoyin sufuri, kafin muka shigo da jam’iyyu da sauran kungiyoyin fararen huda da dai sauransu. Gaba daya dai, muna samun kwarin gwiwa ta hanyar martanin masu ruwa da tsaki a fadin hukumar da irin gudunmawar da suka bayarwa.

“Mun samu matsaloli masu yawa tu daga wurin tantance masu kada kuri’a har zuwa saka sakamakon zabe a na’ura, sai dai mun samu shawarwari a kan haka.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

“Akwai batun kalubalen kai kayayyakin zabe da yadda za a fara zabuka a kan lokaci da da samar da katin zabe da kuma amsa katin da sauransu. Muna samu korafe-korafe masu yawa kuma mun samu shawarwari a kan lamarin, inda wadanda hukumar za ta iya magancesu a ofis, za ta yi hakan, wadanda kuma ke bukatar gyara ga dokokin zabe ne ko kundin tsarin mulki za mu kai su zauren majalisar kasa domin duba lamarin. Don haka mun yi farin ciki da martanin da muka samu da kuma tattaunawa da muka yi a hukumar. Abu mafi muhimmanci ga hukumar shi ne, mun ji ta bakin ‘yan Nijeriya kuma hakan zai ba mu damar komawa kan turbar hukumar domin ci gaba da inganta zaben kasar nan.

“Bayan mun samu wadannan korafe-korafe, hakan zai ba mu damar yin gyare-gyare a zabukan gwamnoni da za su gudana a jihohin Bayelsa, Imo da kuma Kogi a watan Nuwamba, domin za mu kaddamar da wasu daga cikin shawarwarin da muka samu wadanda suka kunshi hukumar, amma wadanda suka kunshi majalisa, majalisar kasa za ta yi aiki ne bisa tanadin dokokin kasar nan.

“Haka kuma akwai wata damar da muka da ita, saboda a halin yanzu kwai zaben cike gurbi har guda hudu da suka hada da mazaba Surulere 1 a Jihar Legas da mazabar Jalingo da ke Jihar Taraba da mazabar Chibok da ke Jihar Borno State da kuma mazabar Chikun da ke Jihar Kaduna. Za mu ci gaba da kaddamar da wasu shawarwarin a zabukan cike gurbi da ke tafe.”

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
El-Rufai Ya Hakura Da Tayin Minista, Ya Zabi Sani Don ya Maye Gurbinsa

El-Rufai Ya Hakura Da Tayin Minista, Ya Zabi Sani Don ya Maye Gurbinsa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.