ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dauki Darasi A Zaben 2023 – Shugaban INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
INEC

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Mahmood Yakubu ya bayyana cewa sun yi matukar daukar darasi a zaben 2023, sannan za su kara kwazo a zaben gwamnoni da zai gudanar a jihohin Kogi, Imo da kuma Bayelsa.

Ya kara da cewa hukumar ta gamsu da irin martanin da ta samu a yayin bitar bayan zaben 2023 da hukumar ta shirya.

  • NSCDC Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 10, Ta Kafa ‘Yan Sintiri
  • Yadda Amurka Ke Kwaton Albarkatun Kasa Da Kasa Da Sunan Yaki Da Ta’addanci

Shugaban INEC ya bayyana hakan ne a jim kadan bayan kammala bitar zaben 2023 na kwanaki uku da ya gudana a Jihar Legas, inda ya tabbatar da cewa za a magance matsalolin da suka faru a lokacin zaben da tare da yin amfani da shawarwarin da hukumar ta samu domin inganta zaben kasar nan, wanda hukumar za ta fara yin gwaji a zabukan gwamnoni da za su gudana a jihohin Kogi, Imo da kuma Bayelsa.

ADVERTISEMENT

“Mun yi wa ‘yan Nijeriya alkawarin cewa za mu gudanar da bitar zaben 2023 a cikin wata daya. Mun fara ne tun daga ranar 4 ga watan Yulin har zuwa 4 ga watan Agusta, mun samu korafe-korafe mai matukar yawan gaske. Mun fara gudanar da taron tattaunawa na shawarwari da kwamishinoninmu da ke jihohi, sannan muka zarce har zuwa wurin kungiyoyin sufuri, kafin muka shigo da jam’iyyu da sauran kungiyoyin fararen huda da dai sauransu. Gaba daya dai, muna samun kwarin gwiwa ta hanyar martanin masu ruwa da tsaki a fadin hukumar da irin gudunmawar da suka bayarwa.

“Mun samu matsaloli masu yawa tu daga wurin tantance masu kada kuri’a har zuwa saka sakamakon zabe a na’ura, sai dai mun samu shawarwari a kan haka.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

“Akwai batun kalubalen kai kayayyakin zabe da yadda za a fara zabuka a kan lokaci da da samar da katin zabe da kuma amsa katin da sauransu. Muna samu korafe-korafe masu yawa kuma mun samu shawarwari a kan lamarin, inda wadanda hukumar za ta iya magancesu a ofis, za ta yi hakan, wadanda kuma ke bukatar gyara ga dokokin zabe ne ko kundin tsarin mulki za mu kai su zauren majalisar kasa domin duba lamarin. Don haka mun yi farin ciki da martanin da muka samu da kuma tattaunawa da muka yi a hukumar. Abu mafi muhimmanci ga hukumar shi ne, mun ji ta bakin ‘yan Nijeriya kuma hakan zai ba mu damar komawa kan turbar hukumar domin ci gaba da inganta zaben kasar nan.

“Bayan mun samu wadannan korafe-korafe, hakan zai ba mu damar yin gyare-gyare a zabukan gwamnoni da za su gudana a jihohin Bayelsa, Imo da kuma Kogi a watan Nuwamba, domin za mu kaddamar da wasu daga cikin shawarwarin da muka samu wadanda suka kunshi hukumar, amma wadanda suka kunshi majalisa, majalisar kasa za ta yi aiki ne bisa tanadin dokokin kasar nan.

“Haka kuma akwai wata damar da muka da ita, saboda a halin yanzu kwai zaben cike gurbi har guda hudu da suka hada da mazaba Surulere 1 a Jihar Legas da mazabar Jalingo da ke Jihar Taraba da mazabar Chibok da ke Jihar Borno State da kuma mazabar Chikun da ke Jihar Kaduna. Za mu ci gaba da kaddamar da wasu shawarwarin a zabukan cike gurbi da ke tafe.”

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
El-Rufai Ya Hakura Da Tayin Minista, Ya Zabi Sani Don ya Maye Gurbinsa

El-Rufai Ya Hakura Da Tayin Minista, Ya Zabi Sani Don ya Maye Gurbinsa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.