ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

El-Rufai Ya Hakura Da Tayin Minista, Ya Zabi Sani Don ya Maye Gurbinsa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
El-Rufai

Tsohon  gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, ya hakura gami da cire ransa daga sha’awar zama minista a karkakashin mulkin shugaba Tinubu kamar yadda jaridar Premium Times ta nakalto.

Wata majiya daga fadar shugaban kasa ta ce, Nasir El-Rufai ya shaida wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu yayin wata ganawa da suka yi a ranar Talata cewa, shi kam yanzu bai da ra’ayin zama minista, amma duk da hakan zai bada tasa gudunmawar wajen cigaban Nijeriya a matsayinsa na dan kasa.

  • Mun Dauki Darasi A Zaben 2023 – Shugaban INEC
  • Sin Ta Kara Ware Yuan Biliyan 1.46 Don Taimakawa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

“Ya shaida wa shugaban kasa cewa ya na son ya maida hankalinsa kan darasin dakta a jami’ar The Netherlands,” a cewar daya daga cikin majiyoyin.

ADVERTISEMENT

Wata majiyar kuma ta shaida cewar tsohon gwamnan ya bada shawarar a zabi Jafaru Ibrahim Sani daga jihar Kaduna a matsayin minista da zai maye gurbin ta’ayin da aka masa da farko, a cewarsa, shugaban kasa zai samesa a matsayin mutum mai matukar amfani.

Shi dai Sani ya yi aiki a matsayin kwamishina a ma’aikatu har uku a karkashin mulkin gwamna Nasiru El-Rufai.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Nasiru dai ya gana da shugaban kasa a fadar shugaban kasa da ke Abuja bayan da majalisar dattawa ta tantance da amincewa da zabin ministoci 45 cikin 48 da shugaban kasa ya aike musu.

Kodayake, majalisar ta ki amince da zabin Nasir El-Rufai da wasu mutum biyu bisa rahoton tsaro da bai amince da su ba.

Sauran mutum biyun da majalisar ta ki amince da nadinsu su ne tsohon sanata daga Taraba, Sani Danladi, da kuma Stella Okotete daga jihar Delta.

Majiyoyin sun ce a lokacin da El-Rufai ya ji matakin da Majalisa ta tsayar kansa yana ma can kasar Landan nan da nan ya dawo Nijeriya a ranar Litinin domin neman ganawa da shugaban kasa kan batun.

A cewar majaliyar a yayin zaman shugaban kasa da El-Rufai, Tinubu ya fada masa cewar ya amshi wasu korafe-korafe a kan nadin da ya amsa na minista.

Sai dai shugaban ya nemi awanni 24 domin ya sake bibiyar korafe-korafen da rahoton tsaro na SSS domin ganin an samu damar da majalisa za ta iya amincewa da shi.

A lokacin ne sai El-Rufai ya amsa da cewa shi yanzu ba ya da ra’ayin zama minista kuma, tun da wasu da suke makale a jikin shugaban kasan ba su da ra’ayin zamansa minista.

Lokacin da aka tuntubi kakakin Malam Nasir, Muyiwa Adekeye, ya ki cewa uffan kan labarin.

El-Rufai
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Matakin Amurka Na Neman Takaita Zuba Jari A Kasar Sin Illata Kai Ne

Matakin Amurka Na Neman Takaita Zuba Jari A Kasar Sin Illata Kai Ne

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.