ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Éric Sékou Chelle: Sabon Kociyan Super Eagles

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
Chelle

A satin da ya gabata ne hukumar kwallon kafar Nijeriya, NFF ta tabbatar da daukar Éric Sékou Chelle a matsayin sabon kocin kungiyar kwallan kafa ta Super Eagles kuma kamar yadda sanarwar ta tabbatar nadin Chelle ya fara aiki ne nan take inda a cewar hukumar NFF ta yanke shawarar daukar sabon kocin ne daga ketare a zaman da ta yi ranar 2 ga watan Janairun wannan shekarar ta 2025.

NFF ta ce babban aikin da ta dora wa tsohon kocin dan asalin kasar Mali shi ne: kai Nijeriya Gasar Kofin Duniya ta 2026, abin da masana kwallon kafa a nahiyar Afirka da ma Nigeriya suke ganin da kamar wuya ganin yadda rukunin da Nigeriya take ciki yake da kuma kalubalen da ke gaban samun tikitin zuwa gasar ta cin kofin duniya da zai fara jagorantar Nigeriya a cikin wannan shekarar.

  • Kar Ku Tayar Da Hankalinku Kan Cutar Tsuntsaye – Ma’aikatar Lafiya Ta Kano
  • Duniya Na Fatan Sin Da Amurka Za Su Cika Alkawuransu Cikin Hadin Gwiwa

Waye Éric Sékou Chelle

ADVERTISEMENT

Ba kamar sauran fitattu a harkar kwallon kafar Afirka, irin su George Weah da Abedi Pele da Samuel Eto’o da Rashidi Yekini da sauransu ba, Eric Chelle ba fitacce ba ne a kwallon kafar Afirka, dalili kuwa shi ne a lokacin da yake dan wasa bai wani shahara sosai ba saboda a lokacin da yake buga wasa, sau biyar kawai ya buga wa babbar tagawar kwallon kwallon kafar kasarsa, Mali wasa. Dangane da matakin kungiyoyi kuwa, ya buga wasa ne yawanci a kananan kungiyoyin Faransa, irin su Martigues da Balenciennes da Lens da Istres da kuma Chamois Niortais. To sai dai Chelle ya bai wa mutane da dama mamaki a matakin koci saboda irin kokarin da ake ganin ya yi domin kafin ya zama kocin babbar tawagar Mali, ya rike wasu kungiyoyin Faransa da ke buga karamar gasar kasar.

Chelle, mai shekara 47 ya samu kwarewa a aikin horarwa ne a kungiyoyin GS Consolat, FC Martigues, MC Oran and Boulogne kuma a shekarar 2022 ce Mali ta nada shi a matsayin wanda zai jagoranci babbar tawagar kasar, kuma ya bayar da mamaki bayan ya kai kasar gasar cin Kofin Afirka ta 2023 da aka gudanar a Ibory Coast inda a gasar ce, Mali ta samu nasarar kai wa matakin kwata-fainal, kafin mai masaukin baki ta fitar da ita a karin lokaci, sai dai bayan gasar ne kasar ta kore shi a watan Yunin 2024.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

‘Rike Super Eagle ba karamin aiki ba ne’

Amma kuma aikin horar da Nijeriya babban aiki ne da ke bukatar kwarewa da jajircewar koci, la’akari da yadda kasar nan ke da fitattun ‘yan wasa da ke buga wasa a wasu manyan kungiyoyin Turai wanda hakan yake nufin ko a wajen gayyatar ‘yan wasa akwai babban aiki a wajen mai koyar da tawagar Nigeriya saboda akwai ‘yan wasa da yawa kuma suna kokarin da ya kamata a gayyace su.

To amma duk da kwararrun ‘yan wasa da kasar nan ke da su, tana fama da matsalar samun nasarorin da ake bukata a wasanninta, musamman a Afirka kuma mutane da alama na alakanta rashin katabus da Super Eagle ke yi da rashin kwararren koci, wanda zai iya hada fitattun ‘yanwasan da kasar ke da su domin hada tawaga mai karfin da za ta lashe babbar gasa.

Masu koyarwa da dama – na ciki da wajen kasar nan sun zo, sun kuma tafi, amma babbar tambayar da ke yawo a bakunan ‘yan Nigeriya, shi ne shin

Eric Chelle zai iya fitar wa Super Eagles kitse daga wuta?

Cikin sanarwar nadin nasa, NFF ta dora masa alhakin kai Nijeriya gasar Kofin Duniya domin a yanzu haka kasar nan na matsayi na biyar a kan teburin neman gurbin shiga gasar Kofin Duniya ta 2026 da maki uku, bayan da ta ji jiki a hannun Benin da Lesotho sannan wasannin farko da Chelle zai fuskanta a neman gurbin Gasar Kofin Duniya ta 2026 su ne a watan Maris inda zai buga wasanni biyu. Amma kuma a yanzu hankula sun koma kan sabon kocin domin ganin irin rawar da zai taka wajen farfado da Super Eagles.

Chelle
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
Tashar Tekun Ningbo-Zhoushan Ta Sin Ta Sake Zama Kan Gaba A Duniya A 2024

Tashar Tekun Ningbo-Zhoushan Ta Sin Ta Sake Zama Kan Gaba A Duniya A 2024

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.