• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fada Ya Barke Tsakanin Shugabannin ’Yan Bindiga, 2 Sun Mutu Yayin Rikicin A Zamfara

by Muhammad
3 years ago
in Al'ajabi
0
Fada Ya Barke Tsakanin Shugabannin ’Yan Bindiga, 2 Sun Mutu Yayin Rikicin A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fadan ‘yan bindigar ya kai ga kashe wasu manyan shugababbin bangarorin biyu da suka hada da Dulhu da kuma Dan Maigari, tare da yaransu sama da 15 a rikici da ya barke tsakaninsu a dajin Zamfara.

Aminiya ta rawaito wani kazamin fadan ya kaure ne a safiyar Talata tsakanin bangaren kasurgumin dan bindiga, Bello Turji da wancan bangaren na ’yan bindigar da suka dade ba sa ga-maciji da juna.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sako Wasu Mutum 2 Da Suka Sace A Wata Cocin Jihar Abiya 
  • Kisan ‘Yan Arewa A Kudu: An Bukaci Gwamnati Ta Gaggauta Daukar Mataki

Wani ganau ya shaida wa Aminiya cewa, “Turji ya yi garkuwa da wadansu mutane, amma mun ji an ce daga baya ya kashe su; an bar gawar Dulhu na da sauran yaransa a maboyarsa.

“Shi kanshi Turji ana kyautata zaton an kashe yaransa a musayar wutar, amma ba a san ko mutum nawa ba ne; amma na ga wadansu daga cikinsu ana komawa da su, dauke da raunin harbi.”

Bangaren Turji da su Dulhu sun yi musayar wutar ne kan zargin kashe wani dan bindiga da ke karkashin wani yaron Bello Turji, wanda ake kira Na-Sanda.

Labarai Masu Nasaba

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Aminiya ta gano a kan haka ne Turji ya jagoranci yaransa suka kai harin ba-zata a maboyar su Dulhu da ke Maniya, inda suka kashe ’yan bindiga da dama.

Daga cikin ’yan bindigar da su Turji suka kashe har da Dulhu da Dan Maigari, wanda kani ne ga Bashari Maniya, tsohon dan bindiga da yanzu ya zama mai shiga tsakani domin sasantawa tsakanin ’yan bindiga da gwamnati.

Ganau a kauyen Dangondi sun shaida wa Aminiya cewa sun ga ’yan bindiga da dama daga Maniya suna tsallaka babban titin Moriki zuwa Shinkafi, domin tserewa da rayuwarsu, ta cikin dajin Sabubu.

Wakilin Aminiya a Gusau ya nemi samu karin bayani daga kakakin ’yan sandan Jihar Zamfara, SP Shehu Muhammad, amma bai amsa kiran waya ko rubutaccen sakon da wakilin namu ya yi mishi ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Yan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Bincike Kan Kisan Mutum 3 A Zaben Fidda Gwani Na APC, An Bukaci Soke Zaben Kano

Next Post

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A Shugabancin Jam’iyyar APC Ta Kasa

Related

Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

9 hours ago
Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
Al'ajabi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

3 months ago
Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
Al'ajabi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

3 months ago
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

4 months ago
An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

4 months ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

4 months ago
Next Post
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A Shugabancin Jam’iyyar APC Ta Kasa

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A Shugabancin Jam'iyyar APC Ta Kasa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.