• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fahimtar Nasarorin Siyasar Jam’iyyar Da Ta Yi Shekaru Dari Da Uku

bySulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Siyasa

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Sama da karni guda ke nan, Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin (JKS) ta hada kan Sinawa wajen raya kasa bisa tsarin gurguzu daidai da dabi’un Sinawa. Manufar jam’iyyar ita ce tabbatar da farin cikin jama’a, da sake farfado da al’ummar kasar, kuma ta samu sakamako na hakika na asali bisa kyawawan manufofin raya kasa. Baya ga nasarorin da suka fi shahara a fannin tattalin arziki da zamantakewa, nasarorin siyasa da jam’iyyar ta samu suna da ban mamaki.  

A ko da yaushe JKS tana bunkasa tsarin siyasar kasar Sin bisa tarihin kasar da yanayin kasa, da tabbatar da ingantacciyar alkiblar ci gaban kasa tare da daidaita bukatun tsarin mulkin kasar bai daya. Tsarin dimokuradiyyar Sin ya kasance tamkar tsintsiya madaurinki daya, hakan ya samo asali ne daga hadewar tsarin da aka shigo da shi daga kasashen waje da kuma salon siyasa ta kasar Sin ta cikin gida, wanda ke ba da damar saukaka yanke shawara mai inganci da ake bukata don ci gaban kasa, tare da tabbatar da hadin kan jam’iyya da dimokuradiyyar zamantakewa.

  • Masana’antar Kera Bayanan Kayayyakin Laturoni Ta Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Bunkasuwa Daga Janairu Zuwa Mayu
  • Kasar Sin Ta Amince Da Dokar Ba Da Agajin Gaggawa Da Aka Yi Wa Kwaskwarima

Tsarin majalisar wakilan jama’ar kasar Sin, wanda shi ne tsarin gudanarwa mai matakai daban-daban dauke da tsarin dokoki, ya dace da tsarin kasar a matsayin kasa mai girma da yawan jama’a, da tabbatar da cewa ikon gwamnati na hannun jama’a. Yayin da taron ba da shawara kan harkokin siyasa na jama’ar kasar Sin, wanda shi ne mafi kololuwar hukumar ba da shawarwari kan harkokin siyasa ga gwamnati, ta kunshi daidaituwa a cikin mabambantan yanayi, wanda ke da tushe mai zurfi a cikin al’adun tarihi da al’adun kasar Sin, da tabbatar da kwanciyar hankali da ci gaba. Duk wadannan hukumomi suna nuna hikima da hangen nesa na JKS wajen tafiyar da mulkin kasar.

Jama’a su ne ginshikin kasa, kuma kasa za ta samu zaman lafiya idan har ginshikinta ta karfafa. Hidimtawa jama’a da zuciya daya shi ne ainihin manufar JKS, yayin da take dagewa kan mutunta ra’ayin jama’a, da kiyaye hakki da moriyar jama’a, da kyautata jin dadin jama’a a harkokin siyasar kasar Sin. Wannan falsafa ita ce ginshikin da ta rike jam’iyyar sama da karni guda ba tare da tangarda ba. (Yahaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
Wata Sabuwa: KEDCO Ta Yanke Wutar Jami’ar Dangote Da Ke Kano 

Wata Sabuwa: KEDCO Ta Yanke Wutar Jami'ar Dangote Da Ke Kano 

LABARAI MASU NASABA

A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version