• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [12]

by Nuhu Ubale Ibrahim
2 months ago
in Addini, Bakon Marubuci, Ilimi
0
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rabe-raben Rai

Ibnu Juzai a-Kalbi Allah Ya yi masa rahama yana cewa:

النُّفُوسُ ثَلَاثَةُ أَنْوَاعٍ: أَمَّارَةٌ بِالسُّوءِ، وَلَوَّامَةٌ، وَهِيَ الَّتِي تَلُومُ صَاحِبَهَا، وَمُطْمَئِنَّةٌ.

Fassara:

“Rai nau’i uku ne: Rai mai umarni da mummuna, da rai mai yawan zargin kanta, wato mai yin tir da ma’abocinta ida ya yi kuskure, da kuma rai mai nutsuwa” Duba Kitãbu at-Tashīlu Li’ulūmi at-Tanzil [2/122]

Labarai Masu Nasaba

An Gano Cushen Biliyan 5 Cikin Kasafin Kuɗin Hukumar Alhazai Ta Ƙasa

Nijeriya Za Ta Karɓi Bakuncin Gasar Karatun Alƙur’ani Mai Girma Ta Duniya

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [10]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [9]

Fashin Baƙi:

Ibn Juzai, ya bayyana nau’ikan rai uku da suka shafi halayyar ɗan’adam, bisa koyarwar addinin Islama. Waɗannan nau’ikan rai suna da nasaba da matsayin mutum a cikin halayensa da alaƙarsa da Allah. Ga cikakken bayani kan kowanne daga cikinsu:

1. Rai Mai Umarni da Mummuna (النَّفْسُ الأَمَّارَةُ بِالسُّوءِ): Wannan ita ce zuciyar da take yawan umartar mai ita da aikata sharri da mugunta, da saɓo. Allah Ya ambaci irin wannan rai a cikin Alƙur’ani inda Ya ce:” Ba kuma ina wanke kaina ba ne. Shakka babu ɗabi’ar rai ce ta umurci mutum da yin mummunan abu, sai fa wanda Ubangiji Ya yi wa jin ƙai. Lalle Ubangiji Mai gafara ne Mai jin ƙai” Suratu Yusuf aya ta 53.

Irin wannan rai tana da alaƙa da sha’awa, da son zuciya, da rinjayen Shaiɗan a kanta. Duk wanda yake a wannan matsayi, yana yawan aikata laifi ba tare da jin kunya ba. Sai dai idan Allah Ya yi masa rahama, zai farka daga halinsa ya nemi gafara ya tuba.

Alamomin Rai Mummuna: Yawan aikata zunubi ba tare da nadama ba.
Jin daɗi da mugunta da zalunci.
Rashin kulawa da umarnin Allah da hani.
Bin son zuciya da jin daɗin duniya fiye da lahira.

Hanyoyin Gyara Irin Wannan Rai:

● Neman gafarar Allah akai-akai.
● Yawan ambaton Allah (zikiri) don rage rinjayen sha’awa.

●Yin hijira daga munanan abokai ko yanayi.
● Cusa wa rai ƙaunar ibada da karatun Alƙur’ani.

2. Rai Mai Yawan Zargin Kanta (النَّفْسُ اللَّوَّامَةُ):
Wannan ita ce zuciyar da take tsawatar da mai ita a lokacin da ya aikata kuskure,ko zai aikata shi. Wannan nau’in rai yana matakin tsaka-tsaki tsakanin mugunta da kyautatawa. Allah Ya ambaci wannan rai a cikin Alƙur’ani, inda Ya ce:” Ina rantsuwa da rai mai yawan zargin kanta.” Suratul Ƙiyama aya ta 2.

Mutumin da yake da wannan rai yana aikata laifi amma daga baya zuciyarsa tana yi masa tir, tana sa shi jin nadama. Wannan nadama ita ce take jawo tuba da gyara hali.

Alamomin Rai Mai Yawan Zargin Kanta:

● Yawan jin laifi da nadama bayan aikata kuskure.
● Farkawa daga barci na gafala idan aka yi laifi.
●Rashin kwanciyar hankali yayin aikata haram.
● Son gyara hali da tuba.

Hanyoyin Ƙarfafa Rai Mai Yawan Zargin Kanta:

● Cusa wa zuciya son Allah da Manzonsa.
● Taimaka wa rai da kyakkyawan abokai.
● Rayuwa a cikin yanayi mai tsafta da ibada.
● Yawan karanta tarihin mutanen kirki don yin koyi da su.

3. Rai Mai Nutsuwa (النَّفْسُ الْمُطْمَئِنَّةُ): Wannan ita ce zuciyar da ta samu cikakken natsuwa da yarda da hukuncin Allah. Wannan mataki ne mafi girma a cikin halayyar rai. Allah Ya ambaci irin wannan rai a Alƙur’ani inda Ya ce:” Ya kai wannan rai mai nutsuwa. Ka koma zuwa ga Ubangijinka kana mai yarda da sakamako abin yarda. Don haka, ka shiga cikin bayina. Ka kuma shiga Aljannata.” Suratul Fajri aya ta 27-30.

Wannan matakin na rai yana ga mutanen da suka sami cikakkiyar ɗa’a da biyayya ga Allah da Manzonsa (S.A.W). Sun tsarkake zukatansu daga son zuciya, da hassada, da riya, da zalunci. Duk wata fitina da ta zo masu, sun yarda da cewa ƙaddarar Allah ce, don haka ba sa firgita ko damuwa.

Alamomin Rai Mai Nutsuwa:

● Tsananin ƙaunar Allah da Manzonsa fiye da komai.
● Cikakkiyar yarda da ƙaddara, mai daɗi ko akasin haka.
● Jin daɗin ibada da guje wa sharri.
● Kyautatawa ga mutane ba tare da neman lada a duniya ba.
● Jin daɗin rayuwa ko da an sami wahala.

Hanyoyin Samun Rai Mai Nutsuwa:

● Yawaita karatun Al-Qur’ani da nazarin ma’anoninsa.
● Yin addu’a don tsarkake zuciya daga cututtukan rai.
● Yawaita tunani a kan lahira da rayuwar gaskiya.
● Gujewa duniya da halayenta marasa amfani.

Waɗannan nau’ikan rai suna nuni da matakin da mutum yake a cikin bautar Allah. Duk wani mai imani yana ƙoƙarin tashi daga rai mai umurni da mummuna zuwa rai mai yawan zargin kanta, sa’an nan zuwa rai mai nutsuwa. Wannan tafiya tana buƙatar dagewa da ibada, sabo da zuciya na da ƙarfi wajen rinjayar hali.

Ibn Juzai Allah Ya yi masa rahama ya bayyana waɗannan matsayin domin su zama ginshiƙin gyara hali da kyautata rayuwa ta ibada. Duk wanda yake aiki da wannan koyarwar, zai iya cimma babban matsayi na kusanci da Allah, wanda a ƙarshe zai kai shi ga samun dacewa da rahama a duniya da lahira.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abu Razina Nuhu Ubale PakiAl-qur'aniAlƙur’aniIbnu JuzaiRamadanTafsiriTafsirin Alƙur’aniTafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Alakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Bisa Daidaito Tsakanin Sin Da Amurka Za Ta Amfanar Da Kamfanonin Duniya

Next Post

Dokar Ta-Ɓaci: Tinubu Ya Kauce Hanya, Ya Ci Zarafin Dimokuraɗiyya A Ribas – Sambauna

Related

An Gano Cushen Biliyan 5 Cikin Kasafin Kuɗin Hukumar Alhazai Ta Ƙasa
Addini

An Gano Cushen Biliyan 5 Cikin Kasafin Kuɗin Hukumar Alhazai Ta Ƙasa

1 day ago
Nijeriya Za Ta Karɓi Bakuncin Gasar Karatun Alƙur’ani Mai Girma Ta Duniya
Addini

Nijeriya Za Ta Karɓi Bakuncin Gasar Karatun Alƙur’ani Mai Girma Ta Duniya

1 week ago
Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
Ilimi

Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China

1 week ago
Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi
Ilimi

Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi

2 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026

2 weeks ago
Nijeriya Ta Biya Bashin Ɗaliban Da Ke Karatu A Ƙasashen Waje
Ilimi

Nijeriya Ta Biya Bashin Ɗaliban Da Ke Karatu A Ƙasashen Waje

2 weeks ago
Next Post
Dokar Ta-Ɓaci: Tinubu Ya Kauce Hanya, Ya Ci Zarafin Dimokuraɗiyya A Ribas – Sambauna

Dokar Ta-Ɓaci: Tinubu Ya Kauce Hanya, Ya Ci Zarafin Dimokuraɗiyya A Ribas - Sambauna

LABARAI MASU NASABA

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.