ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Obi Ya Yi Alkawarin Biyan Kudin Jarrabawar NECO Na Fursunoni 148

by Idris Aliyu Daudawa
7 months ago
Obi

Tsohon dan takarar Shugaban kasa a karkashin jam’iyya Labour Party, Mista Peter Obi, ya yi alkawarin zai biya kudin jarabawar (NECO) na fursunoni 148 wadanda suke zaune a gidajen gyara halin ka a sassa daban daban na Jihar Anambra.

Obi ya bayyana hakan ne bayan da ya gana da wakilan su fursunoni daga Awka, Onitsha, Nnewi da kuma Aguata na Jihar Anambra.

  • Babu Ɗalibin Da Aka Sace A Makarantar St. Peter’s A Nasarawa – ‘Yansanda
  • 2027: Ganduje Ya Gargaɗi Mambobin APC Kan Fara Tallata Masu Neman Takarar Gwamna Da Wuri

Fursunoni wadanda suke rubuta jarabawa NECO, na iya shiga matsala saboda rashin biyan kudaden jarabawar.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda bayanin alkalumma suka nuna wadanda aka kai ma Obi, Awka na da 50, Onitsha 36, Nnewi 25 da kuma Aguata 37, gaba daya fursunoni 148 ke nan.

Kowane dalibi zai biya ₦aira 30,050 a matsayin kudin jarabawa da kuma karin ₦aira 2,000 saboda wani abu daban, hakan yasa kudaden suka kasance Naira 32,050, gaba daya sun kai jimillar ₦aira milyan 4,741.400.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Tsohon gwamnan Jihar Anambra ya ba tawagar wakilan tabbacin cewar zai biya kudaden domin tabbatar da an barsu sun gama rubuta jarabawa ba tare da kawo masu wata matsala ba.

Ya ce zai yi aiki tare da masu ra’aytinsa da kuma magoya bayansa domin a samu dama ta tara kudaden da ake bukata.

“Zan rubuta ma wakilan ranar Litinin domin tabbatar da cewa za’a iya biyan kudin, wanda hakan zai sa fursunonin su ci gaba da rubuta jarabawa.

Tsohon gwamnan ya kara jaddada cewa ilimi ya kasance wani babban abu ne na gyara al’amura masu yawa, ya ce wuraren ko gidajen gyara halinka wasu wurare ne da ake gyara halayen masu laifi ba wai su kasance wuraren da za a rika azabtar da suu ba.Obi,wanda ba da dadewa bane ya kai ziyararar Jami’ar Jihar California, Sacramento, kan wadansu tsare tsare da suka hada da lamarin daya shafi bada shawara kan lamarin karatu da kuma wadanda suke tsare sanadiyar wani laifin da suka aikata, da kuma wasu daidaikun mutane.

Ya nuna rashin jin dadinsa akan yadda ba a bayar da dama ta samun ilimi ga wadanda suke gidan gyara halinka a sassa daban daban na kasa, inda yace ai rashin samun ingantaccen ilimin ne yake sa irin wadanda suke cikin halin aikata laifin da suka dama.

“Idan mutane suka kammala wa’adin gidajen gyara halinka, dole ne su kasance sun samu mallakar abubuwan da za su sa su taimakawa al’umma, da kuma sake sa kansu hanya madaidaiciya domin jin dadin rayuwarsu.

Shugaban Kasa Tinubu Ya Amince Da Kafa Shugabannin Hukumar Kula Da Jami’oi Karo Na 13

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya amince da nada Shugabannin Hukumar kula da Jami’oi ta kasa a karo na 13 (NUC), inda ya amince da Emeritus Farfesa Oluremi Raphael Aina, OFR ,a matsayin Shugaba .

Shugabannin Hukumar da ba’a dade da kaddamarwa ba, a ma’aikatar ilimi ta tarayya tare da Shugabannin hukumar binciken harkokin ilimi, da ci gaba (NERDC), Cibiyar harkokin Malamai ta kasa (NTI), da kuma hukumar ilimin bai daya (UBEC).

A na shi bayanin, Ministan ilimi, Dakta Tunji Maruf Alausa, ya bayyana cewa Shugaban kasa yayi matukar amincewa da su Shugabannin wajen bayar da shawarar data kamata saboda kwarewar da suke da ita,ilimin da suke da shi wajen yiwa Hukumar jagoranci yayin da shi bangaren ilimin yake aiki domin tabbatar da irin kudurin da gwamnatin tarayya take da shi a karkashin jagorancin Tinubu .

Ita ma hukumar kulawa da harkokin jami’oi ta yi maraba da sabbin Shugabannin nata inda ta yi fatan za su tafiyar da ayyukansu fiye da yadda kowa ya k e tsammani ta hanyar samar da nagarta, shigo da wasu abubuwa a fadin Jami; oin da suke illahirin kowane sako da lungu na Nijeriya.

Obi
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Next Post
Ranar Bikin Kasar Noma Ta Duniya: Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Bai Wa Kasar Noma Kariya

Ranar Bikin Kasar Noma Ta Duniya: Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Bai Wa Kasar Noma Kariya

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.