• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [14]

by Nuhu Ubale Ibrahim
6 months ago
in Addini, Bakon Marubuci, Ilimi
0
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ibnu Juzai a-Kalbi Allah Ya yi masa rahama yana cewa:

وَقَالَ بَعْضُ العُلَمَاءِ: الحَسَدُ أَوَّلُ مَعْصِيَةٍ عُصِيَ اللَّهُ بِهَا فِي السَّمَاءِ وَالأَرْضِ، أَمَّا فِي السَّمَاءِ فَحَسَدُ إِبْلِيسَ لِآدَمَ، وَأَمَّا فِي الأَرْضِ فَقَتْلُ قَابِيلَ لِأَخِيهِ هَابِيلَ بِسَبَبِ الحَسَدِ.

Fassara:

“Wasu malamai sun ce: Hassada ita ce laifi na farko da aka yi wa Allah a sama da ƙasa. Amma a sama, Iblis ne ya yi wa Adam hassada, a ƙasa kuma, Ƙabila ne ya kashe ɗan’uwansa Habila saboda hassada.” Duba Kitãbu at-Tashīlu Li’ulūmi at-Tanzil [4/226]

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [10]

Fashin Baƙi:

Labarai Masu Nasaba

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

Maganar da Ibn Juzai ya kawo tana nuna cewa hassada tana daga cikin manyan laifuka na farko da aka yi wa Allah, kuma tana da mummunan tasiri a rayuwar mutum da zamantakewarsa. Ga bayani dalla-dalla:

1. Hassadar Iblis ga Annabi Adam (A.S) a Sama: Lokacin da Allah ya halicci annabi Adam (A.S.) kuma ya ba shi girma, yana da ilimi da matsayi mafi daraja fiye da sauran halittu, Allah ya umurci mala’iku su yi masa sujada. Dukkan mala’iku sun yi biyayya, amma Iblis ya ƙi, yana mai girman kai da hassada ga annabi Adam (A.S).

Dalilin hassadar Iblis ga Annabi Adam: Ya ga cewa Allah ya fifita Adam a kansa. Ya raina Adam saboda an halicce shi daga ƙasa, shi kuma daga wuta. Ya ji haushin cewa zai rasa matsayinsa a wajen Allah.

Sakamakon wannan hassadar, sai Iblis ya zama la’ananne, kuma Allah ya kore shi daga rahama. Wannan yana nuna cewa hassada na iya kai mutum ga yin tawaye ga tsarin Allah wanda hakan halaka ne da taɓewa da hasara a duniya da lahira.

Hassadar Ƙabila ga Habila a Ƙasa: A lokacin Annabi Adam (A.S.), Allah ya karɓi hadayar Habila, amma bai karɓi ta Ƙabila ba. Wannan ya haddasa hassada a zuciyar Ƙabila har ta kai shi ga yin kisan kai na farko a duniya.

Dalilin hassadar Kabila ga Habila: Ya ga cewa Allah ya karɓi hadayar Habila, ba tashi ba. Ya ji haushin cewa Habila na da falala fiye da shi. Bai yarda da hukuncin Allah ba, sai ya lallaɓa har ya kashe ɗan’uwansa.

Sakamakon haka, Ƙabila ya kasance cikin nadama da tozarta, kuma ya zama wanda ya fara kisan kai a duniya.

Darasin da za a koya daga wannan Magana:

1. Hassada tana kai mutum ga zunubi: kamar yadda Iblis ya yi tawaye, Kabila kuma ya kashe ɗan’uwansa.

2. Allah ne ke bayar da daraja: Domin Ya fifita Adam da Habila, ba don wani abu ba sai hikimarsa da falalarsa.

3. Ya kamata mutum ya yarda da ƙaddarar Allah: Domin da Iblis ya yarda da ƙaddara da bai ƙi yin sujjada ga Annabi Adama AS.S) ba.

4. Hassada tana hana mutum albarka: Iblis ya rasa matsayinsa, Ƙabila kuma ya rasa ɗan’uwansa kuma ya shiga baƙin ciki.

A ƙarshe, wannan magana tana ƙarfafa mu, da mu guji hassada, mu gamsu da abin da Allah ya ba mu, domin tana iya rushe duk wata kyakkyawar dangantaka da haifar da halaka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abu Razina Nuhu Ubale PakiAl-qur'aniAlƙur’aniIbnu JuzaiRamadanTafsiriTafsirin Alƙur’aniTafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Ba Da Jawabi A Kwamitin Kare Hakkin Bil’adama Na MDD A Madadin Kungiyar Abokantaka Ta Inganta Hakkin Bil’adama

Next Post

Dangote Zai Gina Sabuwar Masana’antar Siminti A Jihar Ogun

Related

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

6 days ago
ASUU
Ilimi

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

1 week ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

1 week ago
Ranar Hausa: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Bakon Marubuci

Ranar Hausa: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

2 weeks ago
Lambar Yabo Ta CON: Buni Ya Zama Zinare Bashi Da Maboya
Ilimi

NTIC Ta Jinjina Wa Gwamna Buni Kan Taimako A Bangaren Ilimi

2 weeks ago
Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta
Ilimi

Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta

2 weeks ago
Next Post
Efcc

Dangote Zai Gina Sabuwar Masana’antar Siminti A Jihar Ogun

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.