• English
  • Business News
Sunday, June 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [14]

by Nuhu Ubale Ibrahim
3 months ago
in Addini, Bakon Marubuci, Ilimi
0
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ibnu Juzai a-Kalbi Allah Ya yi masa rahama yana cewa:

وَقَالَ بَعْضُ العُلَمَاءِ: الحَسَدُ أَوَّلُ مَعْصِيَةٍ عُصِيَ اللَّهُ بِهَا فِي السَّمَاءِ وَالأَرْضِ، أَمَّا فِي السَّمَاءِ فَحَسَدُ إِبْلِيسَ لِآدَمَ، وَأَمَّا فِي الأَرْضِ فَقَتْلُ قَابِيلَ لِأَخِيهِ هَابِيلَ بِسَبَبِ الحَسَدِ.

Fassara:

“Wasu malamai sun ce: Hassada ita ce laifi na farko da aka yi wa Allah a sama da ƙasa. Amma a sama, Iblis ne ya yi wa Adam hassada, a ƙasa kuma, Ƙabila ne ya kashe ɗan’uwansa Habila saboda hassada.” Duba Kitãbu at-Tashīlu Li’ulūmi at-Tanzil [4/226]

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [10]

Fashin Baƙi:

Labarai Masu Nasaba

Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani – Daurawa

Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata

Maganar da Ibn Juzai ya kawo tana nuna cewa hassada tana daga cikin manyan laifuka na farko da aka yi wa Allah, kuma tana da mummunan tasiri a rayuwar mutum da zamantakewarsa. Ga bayani dalla-dalla:

1. Hassadar Iblis ga Annabi Adam (A.S) a Sama: Lokacin da Allah ya halicci annabi Adam (A.S.) kuma ya ba shi girma, yana da ilimi da matsayi mafi daraja fiye da sauran halittu, Allah ya umurci mala’iku su yi masa sujada. Dukkan mala’iku sun yi biyayya, amma Iblis ya ƙi, yana mai girman kai da hassada ga annabi Adam (A.S).

Dalilin hassadar Iblis ga Annabi Adam: Ya ga cewa Allah ya fifita Adam a kansa. Ya raina Adam saboda an halicce shi daga ƙasa, shi kuma daga wuta. Ya ji haushin cewa zai rasa matsayinsa a wajen Allah.

Sakamakon wannan hassadar, sai Iblis ya zama la’ananne, kuma Allah ya kore shi daga rahama. Wannan yana nuna cewa hassada na iya kai mutum ga yin tawaye ga tsarin Allah wanda hakan halaka ne da taɓewa da hasara a duniya da lahira.

Hassadar Ƙabila ga Habila a Ƙasa: A lokacin Annabi Adam (A.S.), Allah ya karɓi hadayar Habila, amma bai karɓi ta Ƙabila ba. Wannan ya haddasa hassada a zuciyar Ƙabila har ta kai shi ga yin kisan kai na farko a duniya.

Dalilin hassadar Kabila ga Habila: Ya ga cewa Allah ya karɓi hadayar Habila, ba tashi ba. Ya ji haushin cewa Habila na da falala fiye da shi. Bai yarda da hukuncin Allah ba, sai ya lallaɓa har ya kashe ɗan’uwansa.

Sakamakon haka, Ƙabila ya kasance cikin nadama da tozarta, kuma ya zama wanda ya fara kisan kai a duniya.

Darasin da za a koya daga wannan Magana:

1. Hassada tana kai mutum ga zunubi: kamar yadda Iblis ya yi tawaye, Kabila kuma ya kashe ɗan’uwansa.

2. Allah ne ke bayar da daraja: Domin Ya fifita Adam da Habila, ba don wani abu ba sai hikimarsa da falalarsa.

3. Ya kamata mutum ya yarda da ƙaddarar Allah: Domin da Iblis ya yarda da ƙaddara da bai ƙi yin sujjada ga Annabi Adama AS.S) ba.

4. Hassada tana hana mutum albarka: Iblis ya rasa matsayinsa, Ƙabila kuma ya rasa ɗan’uwansa kuma ya shiga baƙin ciki.

A ƙarshe, wannan magana tana ƙarfafa mu, da mu guji hassada, mu gamsu da abin da Allah ya ba mu, domin tana iya rushe duk wata kyakkyawar dangantaka da haifar da halaka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abu Razina Nuhu Ubale PakiAl-qur'aniAlƙur’aniIbnu JuzaiRamadanTafsiriTafsirin Alƙur’aniTafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Ba Da Jawabi A Kwamitin Kare Hakkin Bil’adama Na MDD A Madadin Kungiyar Abokantaka Ta Inganta Hakkin Bil’adama

Next Post

Dangote Zai Gina Sabuwar Masana’antar Siminti A Jihar Ogun

Related

Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani – Daurawa
Addini

Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani – Daurawa

13 hours ago
Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata
Addini

Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata

14 hours ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

1 day ago
Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC
Ilimi

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

6 days ago
Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 
Bakon Marubuci

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

7 days ago
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
Manyan Labarai

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

2 weeks ago
Next Post
Efcc

Dangote Zai Gina Sabuwar Masana’antar Siminti A Jihar Ogun

LABARAI MASU NASABA

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

June 21, 2025
CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

June 21, 2025
Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

June 21, 2025
EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

June 21, 2025
Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna

Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna

June 21, 2025
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

June 21, 2025
Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika

Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika

June 21, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran

Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran

June 21, 2025
Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa

Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa

June 21, 2025
Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

June 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.