ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [14]

by Nuhu Ubale Ibrahim
1 year ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Ibnu Juzai a-Kalbi Allah Ya yi masa rahama yana cewa:

وَقَالَ بَعْضُ العُلَمَاءِ: الحَسَدُ أَوَّلُ مَعْصِيَةٍ عُصِيَ اللَّهُ بِهَا فِي السَّمَاءِ وَالأَرْضِ، أَمَّا فِي السَّمَاءِ فَحَسَدُ إِبْلِيسَ لِآدَمَ، وَأَمَّا فِي الأَرْضِ فَقَتْلُ قَابِيلَ لِأَخِيهِ هَابِيلَ بِسَبَبِ الحَسَدِ.

Fassara:

ADVERTISEMENT

“Wasu malamai sun ce: Hassada ita ce laifi na farko da aka yi wa Allah a sama da ƙasa. Amma a sama, Iblis ne ya yi wa Adam hassada, a ƙasa kuma, Ƙabila ne ya kashe ɗan’uwansa Habila saboda hassada.” Duba Kitãbu at-Tashīlu Li’ulūmi at-Tanzil [4/226]

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [10]

Fashin Baƙi:

LABARAI MASU NASABA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

Maganar da Ibn Juzai ya kawo tana nuna cewa hassada tana daga cikin manyan laifuka na farko da aka yi wa Allah, kuma tana da mummunan tasiri a rayuwar mutum da zamantakewarsa. Ga bayani dalla-dalla:

1. Hassadar Iblis ga Annabi Adam (A.S) a Sama: Lokacin da Allah ya halicci annabi Adam (A.S.) kuma ya ba shi girma, yana da ilimi da matsayi mafi daraja fiye da sauran halittu, Allah ya umurci mala’iku su yi masa sujada. Dukkan mala’iku sun yi biyayya, amma Iblis ya ƙi, yana mai girman kai da hassada ga annabi Adam (A.S).

Dalilin hassadar Iblis ga Annabi Adam: Ya ga cewa Allah ya fifita Adam a kansa. Ya raina Adam saboda an halicce shi daga ƙasa, shi kuma daga wuta. Ya ji haushin cewa zai rasa matsayinsa a wajen Allah.

Sakamakon wannan hassadar, sai Iblis ya zama la’ananne, kuma Allah ya kore shi daga rahama. Wannan yana nuna cewa hassada na iya kai mutum ga yin tawaye ga tsarin Allah wanda hakan halaka ne da taɓewa da hasara a duniya da lahira.

Hassadar Ƙabila ga Habila a Ƙasa: A lokacin Annabi Adam (A.S.), Allah ya karɓi hadayar Habila, amma bai karɓi ta Ƙabila ba. Wannan ya haddasa hassada a zuciyar Ƙabila har ta kai shi ga yin kisan kai na farko a duniya.

Dalilin hassadar Kabila ga Habila: Ya ga cewa Allah ya karɓi hadayar Habila, ba tashi ba. Ya ji haushin cewa Habila na da falala fiye da shi. Bai yarda da hukuncin Allah ba, sai ya lallaɓa har ya kashe ɗan’uwansa.

Sakamakon haka, Ƙabila ya kasance cikin nadama da tozarta, kuma ya zama wanda ya fara kisan kai a duniya.

Darasin da za a koya daga wannan Magana:

1. Hassada tana kai mutum ga zunubi: kamar yadda Iblis ya yi tawaye, Kabila kuma ya kashe ɗan’uwansa.

2. Allah ne ke bayar da daraja: Domin Ya fifita Adam da Habila, ba don wani abu ba sai hikimarsa da falalarsa.

3. Ya kamata mutum ya yarda da ƙaddarar Allah: Domin da Iblis ya yarda da ƙaddara da bai ƙi yin sujjada ga Annabi Adama AS.S) ba.

4. Hassada tana hana mutum albarka: Iblis ya rasa matsayinsa, Ƙabila kuma ya rasa ɗan’uwansa kuma ya shiga baƙin ciki.

A ƙarshe, wannan magana tana ƙarfafa mu, da mu guji hassada, mu gamsu da abin da Allah ya ba mu, domin tana iya rushe duk wata kyakkyawar dangantaka da haifar da halaka.

Daga
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Ilimi

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki
Bakon Marubuci

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

June 12, 2026
A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara
Bakon Marubuci

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

June 12, 2026
Next Post
Efcc

Dangote Zai Gina Sabuwar Masana’antar Siminti A Jihar Ogun

LABARAI MASU NASABA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.