ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [14]

by Nuhu Ubale Ibrahim
1 year ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Ibnu Juzai a-Kalbi Allah Ya yi masa rahama yana cewa:

وَقَالَ بَعْضُ العُلَمَاءِ: الحَسَدُ أَوَّلُ مَعْصِيَةٍ عُصِيَ اللَّهُ بِهَا فِي السَّمَاءِ وَالأَرْضِ، أَمَّا فِي السَّمَاءِ فَحَسَدُ إِبْلِيسَ لِآدَمَ، وَأَمَّا فِي الأَرْضِ فَقَتْلُ قَابِيلَ لِأَخِيهِ هَابِيلَ بِسَبَبِ الحَسَدِ.

Fassara:

ADVERTISEMENT

“Wasu malamai sun ce: Hassada ita ce laifi na farko da aka yi wa Allah a sama da ƙasa. Amma a sama, Iblis ne ya yi wa Adam hassada, a ƙasa kuma, Ƙabila ne ya kashe ɗan’uwansa Habila saboda hassada.” Duba Kitãbu at-Tashīlu Li’ulūmi at-Tanzil [4/226]

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [10]

Fashin Baƙi:

LABARAI MASU NASABA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Maganar da Ibn Juzai ya kawo tana nuna cewa hassada tana daga cikin manyan laifuka na farko da aka yi wa Allah, kuma tana da mummunan tasiri a rayuwar mutum da zamantakewarsa. Ga bayani dalla-dalla:

1. Hassadar Iblis ga Annabi Adam (A.S) a Sama: Lokacin da Allah ya halicci annabi Adam (A.S.) kuma ya ba shi girma, yana da ilimi da matsayi mafi daraja fiye da sauran halittu, Allah ya umurci mala’iku su yi masa sujada. Dukkan mala’iku sun yi biyayya, amma Iblis ya ƙi, yana mai girman kai da hassada ga annabi Adam (A.S).

Dalilin hassadar Iblis ga Annabi Adam: Ya ga cewa Allah ya fifita Adam a kansa. Ya raina Adam saboda an halicce shi daga ƙasa, shi kuma daga wuta. Ya ji haushin cewa zai rasa matsayinsa a wajen Allah.

Sakamakon wannan hassadar, sai Iblis ya zama la’ananne, kuma Allah ya kore shi daga rahama. Wannan yana nuna cewa hassada na iya kai mutum ga yin tawaye ga tsarin Allah wanda hakan halaka ne da taɓewa da hasara a duniya da lahira.

Hassadar Ƙabila ga Habila a Ƙasa: A lokacin Annabi Adam (A.S.), Allah ya karɓi hadayar Habila, amma bai karɓi ta Ƙabila ba. Wannan ya haddasa hassada a zuciyar Ƙabila har ta kai shi ga yin kisan kai na farko a duniya.

Dalilin hassadar Kabila ga Habila: Ya ga cewa Allah ya karɓi hadayar Habila, ba tashi ba. Ya ji haushin cewa Habila na da falala fiye da shi. Bai yarda da hukuncin Allah ba, sai ya lallaɓa har ya kashe ɗan’uwansa.

Sakamakon haka, Ƙabila ya kasance cikin nadama da tozarta, kuma ya zama wanda ya fara kisan kai a duniya.

Darasin da za a koya daga wannan Magana:

1. Hassada tana kai mutum ga zunubi: kamar yadda Iblis ya yi tawaye, Kabila kuma ya kashe ɗan’uwansa.

2. Allah ne ke bayar da daraja: Domin Ya fifita Adam da Habila, ba don wani abu ba sai hikimarsa da falalarsa.

3. Ya kamata mutum ya yarda da ƙaddarar Allah: Domin da Iblis ya yarda da ƙaddara da bai ƙi yin sujjada ga Annabi Adama AS.S) ba.

4. Hassada tana hana mutum albarka: Iblis ya rasa matsayinsa, Ƙabila kuma ya rasa ɗan’uwansa kuma ya shiga baƙin ciki.

A ƙarshe, wannan magana tana ƙarfafa mu, da mu guji hassada, mu gamsu da abin da Allah ya ba mu, domin tana iya rushe duk wata kyakkyawar dangantaka da haifar da halaka.

Daga
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
Next Post
Efcc

Dangote Zai Gina Sabuwar Masana’antar Siminti A Jihar Ogun

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.