ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangote Zai Gina Sabuwar Masana’antar Siminti A Jihar Ogun

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
1 year ago
Efcc

Shugaban kamfanin Dangote Aliko Dangote, ya bayyana shirin gina tashar jirgin ruwa na biliyoyin Daloli a Jihar Ogun, wanda zai kasance mafi girma a Nijeriya.

Ya kuma ce ana gina sabbin layuka biyu masu karfin metric ton miliyan 6.0 a duk shekara na kamfanin siminti a Itori, Jihar Ogun.

  • Chelle Ya Fara Da Ƙafar Dama A Super Eagles
  • El-Rufa’i Ya Yi Kadan Ya Sa Mu Bar Jam’iyyar PDP – Sule Lamido

Dangote ya yi wannan bayani ga majalisar zartarwa ta Jihar Ogun karkashin jagorancin gwamna Prince Dapo Abiodun a wata ziyarar ban girma da suka kai a Abeokuta.

ADVERTISEMENT

Dangote ya ce “ Ya yanke shawarar zuwa ya sanya hannun jari a Jihar Ogun saboda hangen nesan gwamnatin Yarima Dapo Abiodun da kuma tsare-tsare kyawawa wadanda suka mayar da hankali wajen jawo masu zuba jari, da kuma yanayin da masu zuba jari ke ciki a jihar.”

Ya ce Jihar Ogun na daya daga cikin wuraren da ake zuba jari a Nijeriya, inda ta sanya kanta a matsayin masana’antar ‘mai cin gashin kanta a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

A cewarsa, tun da farko mun kau da kai ga barin sanya hannun jari a shiyyar kasuwanci ta Olokola (OKFTZ), amma saboda manufofinku da kuma yanayin da masu zuba jari ke da shi, ina so in ce mun dawo kuma za mu yi aiki tare da gwamnatin jihar don komawa Olokola, kuma ana shirin gina tashar jiragen ruwa mafi girma a kasar.

Da yake karin haske kan ayyukan da kamfanin ke gudanarwa a Jihar, Dangote ya ce sabbin layukan biyu masu karfin metric tan miliyan 6.0 a kowace shekara na kamfanin siminti an gina su a Itori, yayin da kamfanin siminti na metric ton miliyan 12 a kowace shekara kuma yana nan a Ibeshe.

Bayan kammala aikin, Dangote ya ba da tabbacin cewa, jimillar kamfanonin siminti a jihar za su yi makotaka da metric ton miliyan 18 a duk shekara, wanda zai zama jiha ko yanki mafi girma da ke samar da siminti a Afirka.

“Tare da gudunmawar sauran masu samar da siminti a Jihar, Ogun ta kasance a gaban sauran kasashen Afirka a fannin samar da siminti,” in ji shi.

Dangote ya bayyana cewa kamfanin simintin Dangote ne kan gaba wajen samar da siminti a nahiyar Afirka mai karfin metric ton miliyan 52.0 a duk shekara a fadin nahiyar Afirka.

Ya kara da cewa kashi 70 cikin 100 na simintin ana samar da su ne a Nijeriya, inda kamfanin Obajana da ke Jihar Kogi ke samar da metric ton miliyan 16.25 a duk shekara, wanda shi ne mafi girma a Afirka.

Ya ce zuba jarin da ake yi wajen sarrafa kayayyakin ya sa al’ummar kasar nan ta dogara da kanta wajen samar da siminti, kamar yadda kasar nan ta dogara da kanta wajen samar da taki, inda ake samun rarar kayayyakin da ake samu a kasuwannin ketare, wanda hakan ya sa al’ummar kasar ke samun kudaden musanya da ake bukata.

Yayin da yake lura da cewa burin kamfanin shi ne Nijeriya ta dogara da kanta a duk abin da ake samarwa, Dangote ya bayyana cewa a halin yanzu kamfanin yana biyan bukatun cikin gida na ‘Premium Motor Spirit’ (PMS) daga matatar mai 650,000 a kowace rana a Ibeju-Lekki, da kuma tace man jiragen sama da ‘Likuefied Petroleum Gas’ (LPG).

Ya ce, Nijeriya na kokarin farfado da tattalin arziki; Don haka akwai bukatar kamfanoni masu zaman kansu su kara kaimi ga kokarin gwamnati, yana mai ba da tabbacin cewa kamfaninsa zai ci gaba da nuna imaninsa ga al’ummar kasar da jama’arta ta hanyar zuba jari da nufin kawo sauyi ga tattalin arzikin kasar.

Da yake mayar da martani, Gwamna Abiodun ya jaddada cewa da kafa kamfanin siminti na Itori, zai samar da metric ton miliyan shida na siminti a duk shekara, kuma kamfanin da ake da shi na Ibeshe, yana samar da metric ton miliyan 12, don haka samar da siminti a jihar zai kai metric ton miliyan 18 a duk shekara, wanda zai zama mafi girma a samar da siminti a Nijeriya da kuma yankin Sahara.

Gwamnan ya yaba wa kamfanin bisa yadda bai yi kasa a gwiwa ba wajen aiwatar da ayyukan da suka dace na hadin gwiwa a tsakanin al’umma, kamar yadda a halin yanzu yake aikin gina titin ‘Inter-Change-Papalato-Ilaro’, yana mai tabbatar da cewa gwamnatinsa a shirye take ta hada kai da kamfanin domin ci gaban jihar da kasa baki daya.

Dangote
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
Dangote
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Sin Ta Mai Da Martani Kan Takardar Bayani a Kan Manufar “Zuba Jari A Amurka Ta Zamanto Farko”

Trump Ya Bayyana Dalilin Rufe Gidan Rediyon Muryar Amurka

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.