• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Faransa Ta Shirya Bikin Baje Kolin Hanyoyin Bunƙasa Kasuwancin Kayan Abinci A Nijeriya

by Muhammad and Naziru Adam Ibrahim
7 months ago
in Labarai
0
Faransa Ta Shirya Bikin Baje Kolin Hanyoyin Bunƙasa Kasuwancin Kayan Abinci A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gudanar da wani gagarumin biki a ofishin jakadancin Faransa, da ke Abuja don gabatar da dabarun binciken da hukumar raya ƙasashe ta Faransa (AFD), ta ɗauki nauyin ƙarƙashin kulawar wata cibiya mai suna “Semmaris”, da zummar zamanantar da kasuwannin hada-hadar kayan noma a Nijeriya.

An

Tsare-tsaren sun mayar da hankali ne kan samar da wasu muhimman hanyoyi uku a Nijeriya, tare da haɗa yankunan karkara da manyan birane kamar su jihohin Kano zuwa Kaduna, da Legas zuwa Ogun da Ibadan, da ma garin Onitsha zuwa Fatakwal, don rage asarar bayan girbi tare da inganta safarar amfanin gona da bunƙasa samar da abinci ta yadda za a samar da ayyukan yi.

  • An Bukaci Gwamnain Tarayya Ta Sake Inganta Harkokin Amfanin Gona
  • Gudunmawar Da Sin Take Bayarwa Wajen Tabbatar Da Wadatar Abinci A Duniya

Yayin da wakilan cibiyar Semmaris da AFD, ke miƙa rahoton binciken suka yi, ƙaramin ministan noma da samar da abinci, Sanata Aliyu Sabi Abdullahi, ya bayyana gamsuwarsa da shirin tare da jaddada muhimmancinsa wajen ci gaban Nijeriya, da bunƙasa ayyukan noma da samar da abinci wanda ya ce ya yi dai-dai da wani shirin gwamnati haɗin gwuiwa da Bankin duniya.

An

Labarai Masu Nasaba

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Ministan ya yaba da hadin gwuiwar tsakanin Faransa da Nijeriya inda ya jaddada muhimmiyar rawar da noma ke takawa wajen bunkasar tattalin arziki da samar da ayyukan yi wanda ya ce gwamnatin Nijeriya za ta shirin muhimmanci yadda ake buƙata.

Semmaris wanda kamfanin Faransa, ne da ke kula da kasuwar sayar da kayayyaki na Paris da Rungis, ɗaya ne daga cikin manyan masu harƙallar kasuwancin kayan abinci a duniya kuma ya sahara wajen safarar amfanin gonaki da ajiyarsu, inda ake sa ran wannan haɗin gwuiwar tsakanin za ta ƙunshi wasu kamfanoni na Faransa da yawa, tare da amfani da ƙwarewarsu wajen inganta ayyuka da kasuwancin kayan amfanin gona.

An

Aikin ya haɗa da zuba hannun jari wajen zamanantar da hanyoyin samar da kayayyaki da bunƙasa wuraren ajiya da ababen more rayuwa na kasuwa, da kuma himma wajen ƙarfafawa manoma da masu gudanar da kasuwanci damar gogayya a kasuwannin duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DuniyaFaransaKayan AbinciNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Samu Karin Yawan Hannun Jari A Aikin Noma Da Kashi 226 Cikin Wata Uku

Next Post

‘Yansanda Sun Kama Wata Mata Da Laifin Azabtar Da Yara Kanana A Adamawa

Related

Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno
Labarai

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

6 minutes ago
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

1 hour ago
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19
Manyan Labarai

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

2 hours ago
Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu
Labarai

Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

2 hours ago
Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe
Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

11 hours ago
Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano
Labarai

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

14 hours ago
Next Post
Uba Ya Hallaka Dansa Daya Tilo Kan Cacar-baki

'Yansanda Sun Kama Wata Mata Da Laifin Azabtar Da Yara Kanana A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

May 13, 2025
Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

May 12, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

May 12, 2025
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

May 12, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

May 12, 2025
Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

May 12, 2025
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.