ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bukaci Gwamnain Tarayya Ta Sake Inganta Harkokin Amfanin Gona

by Abubakar Abba
2 years ago
Tarayya

An bukaci gwamnatin tarayya ta inganta sake habaka harkokin amfanin gona, domin samun damar fitar da shi zuwa kasashen waje, kana gwamnatin ta fi mayar da hankali kan gudanar da ayyukan da za su kara habaka fannin; baya ga man fetir da kusan shi kadai ake iya fitar da shi zuwa kasashen na ketare.

Wasu kwararru ne suka bayar da wannan shawara, a taron shekara karo na tara; a wajen baje kolin da bankin Zenith ya shirya.

  • Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi
  • Zaben Kananan Hukumomi: Gwamnoni Na Tozarta Dimokuradiyya – Jam’iyyun Adawa

Taken taron shi ne, ‘Fitar da kayan amfanin gona zuwa kasashen, baya ga man fetir; domin kara farfado da fannin’.

ADVERTISEMENT

Sun sanar da cewa, Nijeriya za ta iya amfana da kashi 70 na yawan matasan da ke kasar ta hanyar hada-hadar musaya.

Daya daga cikin kwararrun, Obiora Madu ya ce, “Kashi 70 na yawan al’ummar Nijeriya, matasa ne; wanda hakan ya sanya muke da karfin da za mu iya gudanar da ayyuka masu yawan gaske a kasuwar duniya”.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Madu ya kara da cewa, akwai bukatar kara wayar da kai; domin fadakarwa a kan ayyukan fitar da kaya zuwa kasashen ketare, musamman a kan amfanin gona.

Wata kididdigar tattalin arzikin kasar a zango na biyu ta yi nuni da cewa, jimillar kayan da ba su shafi fannin mai fetir a Nijeriya ba a 2024, ta kai dala 1.2, daidai da Naira biliyan 1.8, wanda hakan ya nuna cewa, ta kai yawan kashi 9.28 na jimillar kayan da aka fitar a cikin wannann shekara.

Haka zalika, bisa fashin bakin da aka yi na wannan kididdiga ta nuna cewa, fannin da bai shafi man fetir ba; shi ne kan gaba wajen ciyar da cibiyoyin hada-hadar kudi na kasar gaba tare da samar da bayanai kan amfanin gona, kasuwanci da kuma kayan da ake sarrafawa.

Fannin da bai shafi man fetir din kuma ba, ya samar da kashi 94.30 ga tattalin arzikin Nijeriya a zango na biyun 2024, wanda ya yi kasa da kashi 93.62 a 2023, hakan ya nuna cewa; ya kai kashi 94.66 sama da wanda aka samu a zango na farko a 2024, da ya kai kashi 93.62.

Shi ma a nasa jawabin, kwamishinan ma’aikatar noma da samar da wadacaccen abinci, Otunba Faseru na Jihar Osun ya sanar da cewa, dole ne Nijeriya ta karfafa mayar da hankali kan noma, domin samun riba.

“Muna da komai da za mu iya habaka fannin aikin noma a wannan kasa, domin kuwa Allah ya albarkace mu da wadatacciyar kasar noma mai kyau, ga shi kuma muna da ruwan da za mu iya yin noma da shi har sau biyu a shekara”.

A jawabinta na maraba, Manajan Darakta kuma babbar jami’a a bankin Zenith, Adaora Umeoji; ta sanar da muhimmancin da ke tattare da fannin da bai shafi harkokin man fetir ba, musamman wajen kara samar da ayyukan yi.

Tarayya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

An Samu Karin Yawan Hannun Jari A Aikin Noma Da Kashi 226 Cikin Wata Uku

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.