ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bukaci Gwamnain Tarayya Ta Sake Inganta Harkokin Amfanin Gona

by Abubakar Abba
2 years ago
Tarayya

An bukaci gwamnatin tarayya ta inganta sake habaka harkokin amfanin gona, domin samun damar fitar da shi zuwa kasashen waje, kana gwamnatin ta fi mayar da hankali kan gudanar da ayyukan da za su kara habaka fannin; baya ga man fetir da kusan shi kadai ake iya fitar da shi zuwa kasashen na ketare.

Wasu kwararru ne suka bayar da wannan shawara, a taron shekara karo na tara; a wajen baje kolin da bankin Zenith ya shirya.

  • Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi
  • Zaben Kananan Hukumomi: Gwamnoni Na Tozarta Dimokuradiyya – Jam’iyyun Adawa

Taken taron shi ne, ‘Fitar da kayan amfanin gona zuwa kasashen, baya ga man fetir; domin kara farfado da fannin’.

ADVERTISEMENT

Sun sanar da cewa, Nijeriya za ta iya amfana da kashi 70 na yawan matasan da ke kasar ta hanyar hada-hadar musaya.

Daya daga cikin kwararrun, Obiora Madu ya ce, “Kashi 70 na yawan al’ummar Nijeriya, matasa ne; wanda hakan ya sanya muke da karfin da za mu iya gudanar da ayyuka masu yawan gaske a kasuwar duniya”.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Madu ya kara da cewa, akwai bukatar kara wayar da kai; domin fadakarwa a kan ayyukan fitar da kaya zuwa kasashen ketare, musamman a kan amfanin gona.

Wata kididdigar tattalin arzikin kasar a zango na biyu ta yi nuni da cewa, jimillar kayan da ba su shafi fannin mai fetir a Nijeriya ba a 2024, ta kai dala 1.2, daidai da Naira biliyan 1.8, wanda hakan ya nuna cewa, ta kai yawan kashi 9.28 na jimillar kayan da aka fitar a cikin wannann shekara.

Haka zalika, bisa fashin bakin da aka yi na wannan kididdiga ta nuna cewa, fannin da bai shafi man fetir ba; shi ne kan gaba wajen ciyar da cibiyoyin hada-hadar kudi na kasar gaba tare da samar da bayanai kan amfanin gona, kasuwanci da kuma kayan da ake sarrafawa.

Fannin da bai shafi man fetir din kuma ba, ya samar da kashi 94.30 ga tattalin arzikin Nijeriya a zango na biyun 2024, wanda ya yi kasa da kashi 93.62 a 2023, hakan ya nuna cewa; ya kai kashi 94.66 sama da wanda aka samu a zango na farko a 2024, da ya kai kashi 93.62.

Shi ma a nasa jawabin, kwamishinan ma’aikatar noma da samar da wadacaccen abinci, Otunba Faseru na Jihar Osun ya sanar da cewa, dole ne Nijeriya ta karfafa mayar da hankali kan noma, domin samun riba.

“Muna da komai da za mu iya habaka fannin aikin noma a wannan kasa, domin kuwa Allah ya albarkace mu da wadatacciyar kasar noma mai kyau, ga shi kuma muna da ruwan da za mu iya yin noma da shi har sau biyu a shekara”.

A jawabinta na maraba, Manajan Darakta kuma babbar jami’a a bankin Zenith, Adaora Umeoji; ta sanar da muhimmancin da ke tattare da fannin da bai shafi harkokin man fetir ba, musamman wajen kara samar da ayyukan yi.

Tarayya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

An Samu Karin Yawan Hannun Jari A Aikin Noma Da Kashi 226 Cikin Wata Uku

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.